• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi ta zargi Sanatoci biyu masu ci daga jihar, Adamu Aliero da kuma Sanata Dokta Yahaya Abdullahi da yi wa Majalisar Dattijai bayanai na hana bukatar da gwamnatin jihar ta yi na maida wa jihar kudaden da ta yi ayyukan wasu titunan tarayya guda biyu a kan kudi Naira Biliyan shida da Naira Miliyan dari bakwai da gwamnatocin baya suka gina a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar ayyuka da sufuri na jihar, Alhaji Abubakar Chika Ladan ne ya bayyana kan a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai kan a Birnin Kebbi, ya ce “An tafka kura-kurai da karya da ke tattare da ikirarin gwamnatin jihar na mayar da kudaden a hanyoyin tarayya, kuma sanatocin biyu sun mayar da shi tamkar wata kasuwa, in ji shi”.

  • Wata Mata Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta Da Tabarya A Bauchi
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 4 Sun Kwato Alburusai A Kaduna

Ya ce babu lokacin da gwamna ko wani jami’in gwamnatin jihar suka yi ikirarin gina hanyoyin biyu ba, “Duk abin da muka yi shi ne bin hakkin jihar na biyan diyya da abin da ya dace a jihar Kebbi kamar yadda aka yi wa wasu jihohi.

“Ba mu san ko wace shaida Sanata Adamu Aliero da Sanata Yahaya Abdullahi suke nema kan batun biyan jihar, shi ne ya bayar da kwangilar daya daga cikin hanyoyin biyu a lokacin da yake gwamna, shi ma ya fadi haka a zaman majalisar dattawa to mene ne hujjar shi na cewa sai mu gabatar da hujjoji aikin da muka yi. Duk takardun hujjojin da ake so suna a gaban Majalisar Dattawa da na wakilai, wacce hujja ake nema kuma”, in ji kwamishinan Abubakar Chika ladan.

Ya kara da cewa tun bayan umarnin da majalisar dattijai ta bayar na cewa jami’an gwamnatin jihar Kebbi su bayyana a gaban kwamitinta mai kula da lamuni da basussuka tare da duk wasu takardu da suka dace, domin kare ikirarin sake biya na gina titunan gwamnatin tarayya guda biyu a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Ya ce bisa ga bayanin, an gina titin tarayya guda biyu, hanya Dabai-Mahuta-Koko mai tsawon kilomita 91 a tsakanin shekarar 2006-2011 a kan kudi N5,070,912,911.47 da gwamnatin Adamu Aliero ta yi, amma gwamnatin Saidu Dakingari ta kammala shi a shekarar 2011.

Haka kuma Malando-Garin, Saidu Dakingari ne ya gina titin Baka -Ngaski-Warra mai tsawon kilomita 42 daga shekarar 2008-2013 tare da gadar mai fadin mita 90 mai tsawon mita 6 akan kudi N2,200,918,185.78.

“Lokacin da wannan gwamnati ta zo a shekarar 2015, ta gano cewa gwamnatin tarayya na mayarwa gwamnatocin jihohin kudaden da jihohin suka gina a yankinsu.

“A shekarar 2016 gwamnatin jihar ta umurci kwamishinan ayyuka na lokacin, Alhaji Atiku Bunu da ya tuntubi ma’aikatar ayyuka ta tarayya da bukaci cewa gwamnatin Abubakar Atiku Bagudu na da son a mayar da kudaden hanyoyin guda biyu da kuma wasu guda uku da suka kai Naira Biliyan 10.08.

“Sai dai ma’aikatar ayyuka ta tarayya za ta iya amincewa da hanyoyin biyu da wanda Aliero da Dakingari suka yi domin mayar da su, domin an yi su ne kafin shekarar 2015 lokacin da gwamnatin tarayya ta ba da umarnin dakatar da gina titunan gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi suka yi, an ba da izinin ne a shekarar 2020.

“Bayan haka ma’aikatar ta ba da yanke shawarar mayar da kudaden gina hanyoyin biyu zuwa Naira biliyan 6.7 kuma an ba da izinin a ranar 7 ga Satumba, 2022,” in ji shi.

Ya ce a rubuce ne jihar ta mutunta gayyatar da majalisar dokokin kasar ta yi mata domin kare ikirarinta. Ya kara da cewa, bisa wasikar da majalisun dokokin kasar biyu suka rubuta wa gwamnatin jihar, an mika dukkan takardun da suka shafi aikin gina hanyoyin zuwa ga majalisar dattawa da ta wakilai a ranar 27 ga Satumba, 2022.

“A ranar 6 ga watan Oktoba, 2022 ne majalisar dokokin kasar ta gayyaci jihar da ta bayyana gaban kwamitocin majalisun biyu, na jagoranci kwamitin mutum hudu zuwa majalisar dattawa da ta wakilai, mun samu nasarar gabatar da kararmu a gaban kwamitin majalisar wanda daga baya ya jagoranci kwamitin. Don amincewa da biyan bashin da majalisar ta yi amma majalisar dattawa ta bukaci mu jira wasu umarni amma ba mu ji su ba har muka dawo Jihar.”

Kwamishinan ya ce majalisar dattijai ta sake ba wa jami’an jihar damar bayyana a gabanta a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022, “Ya kamata a lura da cewa duk takardunmu da suka dace suna hannun kwamitin majalisar,” inji shi.

Daga karshe ya ba da tabbacin bayyana a gaban kwamitin majalisar dattijai don kare abin da kudaden da suke neman gwamnatin tarayya ta biya Jihar Kebbi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukagwamnatiGwamnatin TarayyaKebbiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Nemi Afuwar Atiku Kan Harin Da Aka Kai Wa Tawagarsa A Borno

Next Post

2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

27 minutes ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

16 hours ago
Next Post
2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu

2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.