• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi ta nuna shirinta na hada gwiwa da masanan kasar Masar wajen bunkasa noma da kiwo.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin kwararrun masana ‘yan kasar Masar da suka ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Bagudu ya shaida wa maziyartan nasa cewa, gwamnatin ta shirya tsaf don hadin gwiwa da hadin kai a matsayin muhimman abubuwan ci gaba, inda ya ce jihar Kebbi ta samu tagomashi wajen noma sosai, kuma an bayyana jihar a matsayin jihar ta biyu mafi yawan kiwon dabbobi a kasar nan.

Hakazalika, jihar ta zama hanyar shigar kasashen Afirka ta yamma wajen kiwon dabbobi saboda kyakkyawan wurin da take da iyaka da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin.

Ya kara da cewa, jihar Kebbi ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta bangarori uku da Kwanni a Jamhuriyar Nijar da kuma Maleville a Jamhuriyar Benin kan bunkasa kiwon dabbobi, noma da cinikayya

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Gwamnan ya bayyana al’ummar jihar Kebbi a matsayin masu aiki tukuru kuma a shirye suke su tsara hanyoyin zamani wajen noma da kiwo.

Sanata Bagudu ya yaba wa shugaban kungiyar manoma shinkafa ta kasa RIFAN, Alhaji Aminu Goroyo bisa yadda ya kai ziyarar kwararu masanan kasar Masar a jihar da kuma shirye-shiryen hadin gwiwa kan fannin noma.

Gwamnan ya bayyana karara cewa zababben shugaban kasar Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin dorawa kan nasarorin da aka samu kan farfado da aikin gona don samar da abinci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a matakin kasa.

Shugaban RIFAN na kasa Alhaji Aminu Goronyo tun da farko ya shaida wa gwamnan cewa kwararrun masanan kasar Masar karkashin jagorancin Janar Walid Yahia Soliman Morsy sun shigo jihar Kebbi ne domin hadin gwiwa kan harkokin noma da Kiwon dabbobi.

Goronyo ya nuna cewa kwararrun za su bunkasa kusan kilomita dari tara na filin Fadama a jihar ta hanyar horas da manoma da aiwatar da tsarin noman zamani da fasaha da kuma kwarewa.

Daga nan ya yaba wa Gwamna Atiku Bagudu a matsayinsa na mataimakin shugaban hukumar kula da samar da abinci ta kasa kan bunkasa noma ta yadda kananan manoma da sauran manoma za su samu kudi da noma wanda hakan ya haifar da karuwar amfanin gona da bunkasa tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiMasarNoma Da Kiwo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Next Post

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

44 minutes ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

3 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

4 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

8 hours ago
Next Post
Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

LABARAI MASU NASABA

Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.