• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi ta nuna shirinta na hada gwiwa da masanan kasar Masar wajen bunkasa noma da kiwo.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin kwararrun masana ‘yan kasar Masar da suka ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Bagudu ya shaida wa maziyartan nasa cewa, gwamnatin ta shirya tsaf don hadin gwiwa da hadin kai a matsayin muhimman abubuwan ci gaba, inda ya ce jihar Kebbi ta samu tagomashi wajen noma sosai, kuma an bayyana jihar a matsayin jihar ta biyu mafi yawan kiwon dabbobi a kasar nan.

Hakazalika, jihar ta zama hanyar shigar kasashen Afirka ta yamma wajen kiwon dabbobi saboda kyakkyawan wurin da take da iyaka da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin.

Ya kara da cewa, jihar Kebbi ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta bangarori uku da Kwanni a Jamhuriyar Nijar da kuma Maleville a Jamhuriyar Benin kan bunkasa kiwon dabbobi, noma da cinikayya

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Gwamnan ya bayyana al’ummar jihar Kebbi a matsayin masu aiki tukuru kuma a shirye suke su tsara hanyoyin zamani wajen noma da kiwo.

Sanata Bagudu ya yaba wa shugaban kungiyar manoma shinkafa ta kasa RIFAN, Alhaji Aminu Goroyo bisa yadda ya kai ziyarar kwararu masanan kasar Masar a jihar da kuma shirye-shiryen hadin gwiwa kan fannin noma.

Gwamnan ya bayyana karara cewa zababben shugaban kasar Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin dorawa kan nasarorin da aka samu kan farfado da aikin gona don samar da abinci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a matakin kasa.

Shugaban RIFAN na kasa Alhaji Aminu Goronyo tun da farko ya shaida wa gwamnan cewa kwararrun masanan kasar Masar karkashin jagorancin Janar Walid Yahia Soliman Morsy sun shigo jihar Kebbi ne domin hadin gwiwa kan harkokin noma da Kiwon dabbobi.

Goronyo ya nuna cewa kwararrun za su bunkasa kusan kilomita dari tara na filin Fadama a jihar ta hanyar horas da manoma da aiwatar da tsarin noman zamani da fasaha da kuma kwarewa.

Daga nan ya yaba wa Gwamna Atiku Bagudu a matsayinsa na mataimakin shugaban hukumar kula da samar da abinci ta kasa kan bunkasa noma ta yadda kananan manoma da sauran manoma za su samu kudi da noma wanda hakan ya haifar da karuwar amfanin gona da bunkasa tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiMasarNoma Da Kiwo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Next Post

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

5 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

7 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

8 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

9 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

10 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.