ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Gwamnatin Jihar Kebbi ta nuna shirinta na hada gwiwa da masanan kasar Masar wajen bunkasa noma da kiwo.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin kwararrun masana ‘yan kasar Masar da suka ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Bagudu ya shaida wa maziyartan nasa cewa, gwamnatin ta shirya tsaf don hadin gwiwa da hadin kai a matsayin muhimman abubuwan ci gaba, inda ya ce jihar Kebbi ta samu tagomashi wajen noma sosai, kuma an bayyana jihar a matsayin jihar ta biyu mafi yawan kiwon dabbobi a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, jihar ta zama hanyar shigar kasashen Afirka ta yamma wajen kiwon dabbobi saboda kyakkyawan wurin da take da iyaka da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin.

Ya kara da cewa, jihar Kebbi ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta bangarori uku da Kwanni a Jamhuriyar Nijar da kuma Maleville a Jamhuriyar Benin kan bunkasa kiwon dabbobi, noma da cinikayya

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Gwamnan ya bayyana al’ummar jihar Kebbi a matsayin masu aiki tukuru kuma a shirye suke su tsara hanyoyin zamani wajen noma da kiwo.

Sanata Bagudu ya yaba wa shugaban kungiyar manoma shinkafa ta kasa RIFAN, Alhaji Aminu Goroyo bisa yadda ya kai ziyarar kwararu masanan kasar Masar a jihar da kuma shirye-shiryen hadin gwiwa kan fannin noma.

Gwamnan ya bayyana karara cewa zababben shugaban kasar Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin dorawa kan nasarorin da aka samu kan farfado da aikin gona don samar da abinci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a matakin kasa.

Shugaban RIFAN na kasa Alhaji Aminu Goronyo tun da farko ya shaida wa gwamnan cewa kwararrun masanan kasar Masar karkashin jagorancin Janar Walid Yahia Soliman Morsy sun shigo jihar Kebbi ne domin hadin gwiwa kan harkokin noma da Kiwon dabbobi.

Goronyo ya nuna cewa kwararrun za su bunkasa kusan kilomita dari tara na filin Fadama a jihar ta hanyar horas da manoma da aiwatar da tsarin noman zamani da fasaha da kuma kwarewa.

Daga nan ya yaba wa Gwamna Atiku Bagudu a matsayinsa na mataimakin shugaban hukumar kula da samar da abinci ta kasa kan bunkasa noma ta yadda kananan manoma da sauran manoma za su samu kudi da noma wanda hakan ya haifar da karuwar amfanin gona da bunkasa tattalin arziki.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.