ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Gwamnatin Jihar Kebbi ta nuna shirinta na hada gwiwa da masanan kasar Masar wajen bunkasa noma da kiwo.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin kwararrun masana ‘yan kasar Masar da suka ziyarce shi a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Bagudu ya shaida wa maziyartan nasa cewa, gwamnatin ta shirya tsaf don hadin gwiwa da hadin kai a matsayin muhimman abubuwan ci gaba, inda ya ce jihar Kebbi ta samu tagomashi wajen noma sosai, kuma an bayyana jihar a matsayin jihar ta biyu mafi yawan kiwon dabbobi a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, jihar ta zama hanyar shigar kasashen Afirka ta yamma wajen kiwon dabbobi saboda kyakkyawan wurin da take da iyaka da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin.

Ya kara da cewa, jihar Kebbi ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta bangarori uku da Kwanni a Jamhuriyar Nijar da kuma Maleville a Jamhuriyar Benin kan bunkasa kiwon dabbobi, noma da cinikayya

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Gwamnan ya bayyana al’ummar jihar Kebbi a matsayin masu aiki tukuru kuma a shirye suke su tsara hanyoyin zamani wajen noma da kiwo.

Sanata Bagudu ya yaba wa shugaban kungiyar manoma shinkafa ta kasa RIFAN, Alhaji Aminu Goroyo bisa yadda ya kai ziyarar kwararu masanan kasar Masar a jihar da kuma shirye-shiryen hadin gwiwa kan fannin noma.

Gwamnan ya bayyana karara cewa zababben shugaban kasar Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin dorawa kan nasarorin da aka samu kan farfado da aikin gona don samar da abinci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a matakin kasa.

Shugaban RIFAN na kasa Alhaji Aminu Goronyo tun da farko ya shaida wa gwamnan cewa kwararrun masanan kasar Masar karkashin jagorancin Janar Walid Yahia Soliman Morsy sun shigo jihar Kebbi ne domin hadin gwiwa kan harkokin noma da Kiwon dabbobi.

Goronyo ya nuna cewa kwararrun za su bunkasa kusan kilomita dari tara na filin Fadama a jihar ta hanyar horas da manoma da aiwatar da tsarin noman zamani da fasaha da kuma kwarewa.

Daga nan ya yaba wa Gwamna Atiku Bagudu a matsayinsa na mataimakin shugaban hukumar kula da samar da abinci ta kasa kan bunkasa noma ta yadda kananan manoma da sauran manoma za su samu kudi da noma wanda hakan ya haifar da karuwar amfanin gona da bunkasa tattalin arziki.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

Tsaka-mai-wuyar Da Zaben 2023 Ya Jefa Bangaren Shari’a

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.