ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya za ta dakatar da ciyar da sama da fursunoni 75,507 da ke gidajen yari 244 a kasar nan daga ranar 31 ga watan Disamban 2023 yayin da gwamnatin jihohi kuma ake tsammanin za su fara ciyar da masu laifin a jihohinsu kai tsaye.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, shi ne ya shelanta hakan a jiya sa’ilin da ke kaddamar da shalkwatar hukumar kula da gidajen yari (NCoS) a Owerri da ke Jihar Imo.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
  • Gawar Wani Tsoho Mai Shekara 115 Ta Yi Batan Dabo A Anambra

Aregbesola, ya ce, kashi 90 cikin 100 na fursunonin da ake da su, mutane ne da suka yi laifi wa jiharsu, don haka lokaci ya yi da jihohi za su fara zuba kudade su na ciyar da masu laifinsu.

ADVERTISEMENT

Wannan bayanin na zuwa ne kasa da awa 24 da gwamnatin tarayya ta fito ta ce, tana kashe naira biliyan N22.4 wajen ciyar da fursunoni a fadin kasar nan, kuma har an shigar da hakan cikin kasafin kudin 2023.

Ya hakikance kan cewa matakin zai taimaka wajen rage cinkoson fursunoni a gidajen yarin kasar nan, Aregbesola ya na mai karawa da cewa kaso 80 na fursunoni su na zaman jiran shari’a ne.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Ya ce, akwai bukatar a sake waiwaye sosai kan tsarin shari’a a fadin kasar nan ta yadda za a ke yanke wa masu jiran shari’a hukunci a kan lokaci da daure wadanda suka dace.

A fadinsa, gwamnatin shugaba Buhari ta yi kokari sosai wajen gyara tsare-tsaren tafiyar da gidajen yari ta hanyar kara kudin da ake kashewa, kwaskwarima wa gidajen yari da kuma gina wasu sabbi dukka a kokarin rage yawan cunkoso.

Ministan ya kara da cewa, “Babban kalubalenmu shi ne yawan cinkoson fursunoni a gidajen yari, musamman a biranen da ke da yawan jama’a da yadda mu’amalar jama’a ke karuwa, don haka aikata laifuka zai karu a wannan wajen don haka ne sai ta kai an ajiye wasu a gidajen yari.

“Mun yi kokarin shawo kan wannan matsalar ta hanyar gina manyan gidajen yari guda shida a shiyyoyi shida da suke fadin kasar nan. Na Kano da na Abuja tunin aka kammala su, sauran ma za a kammala.”

Ya nanata cewa akwai gayar bukatar gyara kan tsarin shari’a ta yadda za a yi waiwaye ga dukkanin abubuwan da suke haifar da jinkirin shari’a domin a cewarsa kaso 70 zuwa ma 80 suna zaman jiran shari’a wanda hakan ba daidai ba ne, “Domin na tabbata a wasu lokutan ana tsare wadanda ma basu da laifi a yi ta ajiyesu a gidajen yari, ta hanyar gudanar da shari’a cikin hanzari ne za a gano mai laifi a yanke masa hukunci wanda bai da laifi a sake shi.”

“Wasu kuma koda sun yi laifin, hukuncin da za a yanke musu bai wuce watanni shida ba ya danganta da laifukan da suka aikata. To amma idan ba a yi shari’a ba sai mutum ya shafe tsawon lokaci a tsare.”

“Jihohi su tashi tsaye su gyara sashin shari’arsu su tabbatar ana yanke hukunci a kan lokaci da hanzarin yin shari’a. Wannan zai taimaka sosai wajen wanzar da adalci da kuma kawo karshen zare wanda ake zargi in ya yi laifi kuma a hukunta shi, in bai yi ba a sake shi,” ya shaida.

Gwamnatin Tarayya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.