ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya za ta dakatar da ciyar da sama da fursunoni 75,507 da ke gidajen yari 244 a kasar nan daga ranar 31 ga watan Disamban 2023 yayin da gwamnatin jihohi kuma ake tsammanin za su fara ciyar da masu laifin a jihohinsu kai tsaye.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, shi ne ya shelanta hakan a jiya sa’ilin da ke kaddamar da shalkwatar hukumar kula da gidajen yari (NCoS) a Owerri da ke Jihar Imo.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
  • Gawar Wani Tsoho Mai Shekara 115 Ta Yi Batan Dabo A Anambra

Aregbesola, ya ce, kashi 90 cikin 100 na fursunonin da ake da su, mutane ne da suka yi laifi wa jiharsu, don haka lokaci ya yi da jihohi za su fara zuba kudade su na ciyar da masu laifinsu.

ADVERTISEMENT

Wannan bayanin na zuwa ne kasa da awa 24 da gwamnatin tarayya ta fito ta ce, tana kashe naira biliyan N22.4 wajen ciyar da fursunoni a fadin kasar nan, kuma har an shigar da hakan cikin kasafin kudin 2023.

Ya hakikance kan cewa matakin zai taimaka wajen rage cinkoson fursunoni a gidajen yarin kasar nan, Aregbesola ya na mai karawa da cewa kaso 80 na fursunoni su na zaman jiran shari’a ne.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce, akwai bukatar a sake waiwaye sosai kan tsarin shari’a a fadin kasar nan ta yadda za a ke yanke wa masu jiran shari’a hukunci a kan lokaci da daure wadanda suka dace.

A fadinsa, gwamnatin shugaba Buhari ta yi kokari sosai wajen gyara tsare-tsaren tafiyar da gidajen yari ta hanyar kara kudin da ake kashewa, kwaskwarima wa gidajen yari da kuma gina wasu sabbi dukka a kokarin rage yawan cunkoso.

Ministan ya kara da cewa, “Babban kalubalenmu shi ne yawan cinkoson fursunoni a gidajen yari, musamman a biranen da ke da yawan jama’a da yadda mu’amalar jama’a ke karuwa, don haka aikata laifuka zai karu a wannan wajen don haka ne sai ta kai an ajiye wasu a gidajen yari.

“Mun yi kokarin shawo kan wannan matsalar ta hanyar gina manyan gidajen yari guda shida a shiyyoyi shida da suke fadin kasar nan. Na Kano da na Abuja tunin aka kammala su, sauran ma za a kammala.”

Ya nanata cewa akwai gayar bukatar gyara kan tsarin shari’a ta yadda za a yi waiwaye ga dukkanin abubuwan da suke haifar da jinkirin shari’a domin a cewarsa kaso 70 zuwa ma 80 suna zaman jiran shari’a wanda hakan ba daidai ba ne, “Domin na tabbata a wasu lokutan ana tsare wadanda ma basu da laifi a yi ta ajiyesu a gidajen yari, ta hanyar gudanar da shari’a cikin hanzari ne za a gano mai laifi a yanke masa hukunci wanda bai da laifi a sake shi.”

“Wasu kuma koda sun yi laifin, hukuncin da za a yanke musu bai wuce watanni shida ba ya danganta da laifukan da suka aikata. To amma idan ba a yi shari’a ba sai mutum ya shafe tsawon lokaci a tsare.”

“Jihohi su tashi tsaye su gyara sashin shari’arsu su tabbatar ana yanke hukunci a kan lokaci da hanzarin yin shari’a. Wannan zai taimaka sosai wajen wanzar da adalci da kuma kawo karshen zare wanda ake zargi in ya yi laifi kuma a hukunta shi, in bai yi ba a sake shi,” ya shaida.

Gwamnatin Tarayya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.