• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya sayo motoci masu aiki da lantarki, inda ya ce “matakin na nufin mazauna Legas za su daina aiki da man fetur su soma amfani da makamashi mai tsafta.”

Gwamnatin Jihar Legas ta ce ta sayo sabbin motoci masu amfani da larntarki da zummar yin aiki da su a matsayin motocin haya.

  • ‘Yan IPOB 9 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Kashe ‘Yansanda A Imo
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Makamai A Zamfara

Gwamnan Jihar, Babajide Sanwo-olu ne ya bayyana haka a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi.

Ya ce an sayo motocin ne da zummar saukaka sufuri da kuma sake tasirin sauyin yanayi a Legas, birni mafi girma a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 15.

Wannan ne karon farko da hukumomi a Nijeriya suka sanar da sayo irin wadannan motoci domin yin sufuri.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

Sanwo-Olu ya ce matakin zai tabbatar da ”tsaftace tsarin sufuri” a jihar.

”Sabbin motocinmu masu aiki da lantarki za su inganta sufuri da kuma rage gurbata muhalli.

Hakan na nufin mazauna jihar za su yi murna da amfani da man fetur sannan su yi maraba da makamashi mai tsafta,” a cewar gwamnan a sanarwar da ya fitar.

Kawo yanzu ba a san adadin motocin da gwamnatin ta saya ba, amma Sanwo-olu ya ce za a karo motoci masu yawa da ke aiki da lantarki don inganta sufuri a jihar

Ya kara da cewa nan da watanni masu zuwa za a soma amfani da motocin a “matakin gwaji.”

A cewarsa hakan zai bai wa gwamnati damar ”tattara isassun bayanai game da aiki da makamashi maras gurbata muhalli” da kuma kwatanta shi da yadda ake sufuri da masu aiki da fetur da zummar inganta tsarin sufuri.

Mutanen jihar sun yi maraba da wanna mataki ko da yake wasu sun nuna dari-dari game da dorewarsa ganin yadda shirye-shirye da dama da gwamnatoci ke bijirowa da su suke lalacewa.

Nijeriya ta yi kaurin suna wurin dauke wutar lantarki don haka mutane ke ganin zai yi wahala matakin ya dore.

Wasu kuma sun bayyana cewa cunkoson ababen hawar da ake fama da shi a Legas zai zama kalubale ga wannan shiri.

Sai dai gwamnati ta ce za ta samar da “tashoshin da za a rika yin cajin motoci masu aiki da lantarkin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babajide Sanwo OluBasLantarkiLegasMotoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Yawaitar Tafiye Tafiye Da Tagomashi A Bangaren Yawon Bude Ido Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Kwanaki 5 A Kasar Sin

Next Post

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Related

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

46 minutes ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

1 hour ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

5 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

20 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

22 hours ago
Next Post
Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.