• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya sayo motoci masu aiki da lantarki, inda ya ce “matakin na nufin mazauna Legas za su daina aiki da man fetur su soma amfani da makamashi mai tsafta.”

Gwamnatin Jihar Legas ta ce ta sayo sabbin motoci masu amfani da larntarki da zummar yin aiki da su a matsayin motocin haya.

  • ‘Yan IPOB 9 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Kashe ‘Yansanda A Imo
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Makamai A Zamfara

Gwamnan Jihar, Babajide Sanwo-olu ne ya bayyana haka a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi.

Ya ce an sayo motocin ne da zummar saukaka sufuri da kuma sake tasirin sauyin yanayi a Legas, birni mafi girma a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 15.

Wannan ne karon farko da hukumomi a Nijeriya suka sanar da sayo irin wadannan motoci domin yin sufuri.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Sanwo-Olu ya ce matakin zai tabbatar da ”tsaftace tsarin sufuri” a jihar.

”Sabbin motocinmu masu aiki da lantarki za su inganta sufuri da kuma rage gurbata muhalli.

Hakan na nufin mazauna jihar za su yi murna da amfani da man fetur sannan su yi maraba da makamashi mai tsafta,” a cewar gwamnan a sanarwar da ya fitar.

Kawo yanzu ba a san adadin motocin da gwamnatin ta saya ba, amma Sanwo-olu ya ce za a karo motoci masu yawa da ke aiki da lantarki don inganta sufuri a jihar

Ya kara da cewa nan da watanni masu zuwa za a soma amfani da motocin a “matakin gwaji.”

A cewarsa hakan zai bai wa gwamnati damar ”tattara isassun bayanai game da aiki da makamashi maras gurbata muhalli” da kuma kwatanta shi da yadda ake sufuri da masu aiki da fetur da zummar inganta tsarin sufuri.

Mutanen jihar sun yi maraba da wanna mataki ko da yake wasu sun nuna dari-dari game da dorewarsa ganin yadda shirye-shirye da dama da gwamnatoci ke bijirowa da su suke lalacewa.

Nijeriya ta yi kaurin suna wurin dauke wutar lantarki don haka mutane ke ganin zai yi wahala matakin ya dore.

Wasu kuma sun bayyana cewa cunkoson ababen hawar da ake fama da shi a Legas zai zama kalubale ga wannan shiri.

Sai dai gwamnati ta ce za ta samar da “tashoshin da za a rika yin cajin motoci masu aiki da lantarkin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babajide Sanwo OluBasLantarkiLegasMotoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Yawaitar Tafiye Tafiye Da Tagomashi A Bangaren Yawon Bude Ido Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Kwanaki 5 A Kasar Sin

Next Post

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

12 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.