ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Neja Ta Bayar Umarnin Kama Duk Wanda Ya Ki Karbar Tsofaffin Kudi

by Sadiq
3 years ago
Neja

Gwamnatin Jihar Neja ta umarci ‘yansanda da sauran jami’an tsaro a jihar da su kama mutanen da suka ka ki karbar tsofaffin kudi.

Sakataren gwamnatin Jihar Neja, Alh. Ahmed Ibrahim Matane, ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a Minna a ranar Litinin.

  • Gwamnatina Za Ta Tabbatar An Fara Hako Mai A Bauchi Da Gombe – Tinubu
  • Burundi Ta Jinjinawa Kwararrun Sin Bisa Tallafin Su A Fannin Raya Aikin Gona

Ya bayyana cewa har yanzu tsofaffin takardun Naira na nan daram kuma duk wanda aka kama ya ki karbarsu domin yin kasuwanci to zai fuskanci fushin doka.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, “Tsoffin takardun Naira na nan daram kuma duk wanda aka kama ya ki karba yana jawo wa ‘yan kasa wahala za a kama shi kuma a gurfanar da shi a gaban kuliya.”

Daga nan sai Matane ya bukaci al’ummar jihar da su gudanar da harkokinsu na yau da kullum sannan su kai rahoton duk mutumin da ya ki karban kudin tsofaffin kudin ga jami’an tsaro a jihar domin daukar matakin da ya dace.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Rashin samun sabbin takardun kudin da aka canja ya janyo wa jama’a kunci, ganin yadda ‘yan kasuwa suka ki karbar tsofaffin takardun naira, tare da dagewa a kan sabbi a matsayin hanyar musayar kudi.

Wasu mazauna yankin da suka zanta da wakilinmu, sun koka da irin wahalhalun da tsarin ya haifar, inda suka yi kira ga gwamnatin jihar da ta tashi tsaye domin rage radadin da jama’a ke ciki.

Wannan dai na zuwa ne bayan wa’adi na biyu da CBN da Gwamnatin Tarayya suka ware na ranar 10 ga watan Fabrairu, 2023 na daina amfani da tsofaffin kudin.

Amma wata kotun koli ta dakatar da su kan cikar wa’adin da suka ware na daina amfani da tsofaffin takardun kudin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Afirka Ta Kudu 

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Afirka Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.