• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa’a A Aikin Jarida – Minista

by Sulaiman
5 months ago
Minista

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana ƙudirin ta na amfani da Ƙirƙirarrar Basira (AI) a aikin jarida cikin ɗa’a, tare da mayar da hankali kan ‘yancin faɗin albarkacin baki, bin ƙa’idojin aikin jarida da kuma koyar da jama’a ilimin kafafen watsa labarai.

 

An ƙarfafa wannan ƙudiri ne a taron bikin Ranar ‘Yancin Jarida ta Duniya na shekarar 2025, wanda aka gudanar a otal ɗin Sheraton da ke Abuja a ranar Juma’a, ƙarƙashin jagorancin Konrad Adenauer Stiftung (KAS) da Cibiyar Ƙirƙire-Ƙirƙiren Jarida da Cigaba (CJID).

  • Xi Ya Bukaci Matasa Da Su Ba Da Gudummawar Cimma Nasarar Zamanantar Da Kasa
  • Babu Dalilin Da Zai Sanya Wasu Mambobin PDP Ficewa A Jam’iyyar A Bauchi

Taken taron shi ne: “Rahoto a Sabuwar Duniya – Tasirin AI Kan ‘Yancin Jarida da Kafafen Yaɗa Labarai,” inda aka tattauna yadda Ƙirƙirar Basira take sauya salon aikin jarida da ƙalubalen da ke tattare da hakan.

 

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

A cikin jawabin sa a taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wasu manyan fa’idoji da kuma irin barazanar da ke tattare wajen amfani da AI a cikin ɗakunan buga labarai.

 

Ya ce duk da cewa AI na taimaka wa ‘yan jarida a Nijeriya wajen saurin bayar da rahoto, da nazarin bayanai da gudanar da bincike, yana da matuƙar muhimmanci a yi amfani da wannan sabuwar fasahar cikin hankali da bin ƙa’idoji.

 

Ya ce: “A yayin da muke rungumar aikin jarida da fasahar AI, dole ne mu tabbatar da cewa ba za a tauye ‘yancin jarida ba, illa ma a ƙara ƙarfafa shi.”

 

Ministan ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta kafa Cibiyar Ilimin Kafafen Watsa Labarai ta UNESCO a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN), inda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya riga ya amince da kuɗin kafa cibiyar.

 

Ana sa ran wannan cibiyar za ta kasance cibiyar ƙasa da ƙasa da za ta inganta aikace-aikacen kafafen watsa labarai cikin gaskiya da tunani mai zurfi a fannin dijital.

 

Haka kuma, ya bayyana cewa Nijeriya tana kan hanyar ƙaddamar da tsarin dokar ƙasa kan amfani da AI a cikin aikin jarida.

 

Wannan tsari zai ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire amma ba tare da tauye ‘yancin jarida ko karya ƙa’idojin aikin ba.

 

Idris ya buƙaci haɗin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, da masana fasaha, da kafafen yaɗa labarai, da ‘yan siyasa da ƙungiyoyin farar hula domin samar da ƙa’idojin amfani da AI, da koyar da sababbin dabaru, da tabbatar da gaskiya, da kuma faɗakar da al’umma.

 

A nata jawabin, Marija Peran, wakiliyar KAS a Nijeriya, ta jaddada irin damar da AI ke bayarwa ga aikin jarida, tare da yin kashedi kan haɗurran da ke tattare da hakan.

 

Ta ce: “Yana da muhimmanci mu kare ‘yancin kafafen yaɗa labarai a duk duniya, musamman yanzu da AI ke ƙara shiga aikin jarida.

 

“A matsayin ta na ƙungiya mai kishin dimokiraɗiyya da doka da oda, KAS tana tare da kafafen yaɗa labarai wajen fuskantar wannan sabon yanayi.”

 

Taron ya samu halartar mutane daban-daban, ciki har da Shugaban Kwamitin Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Majalisar Wakilai, Honarable Akintunde Rotimi Jr.; da wakilan kafafen yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.