ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa’a A Aikin Jarida – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana ƙudirin ta na amfani da Ƙirƙirarrar Basira (AI) a aikin jarida cikin ɗa’a, tare da mayar da hankali kan ‘yancin faɗin albarkacin baki, bin ƙa’idojin aikin jarida da kuma koyar da jama’a ilimin kafafen watsa labarai.

 

An ƙarfafa wannan ƙudiri ne a taron bikin Ranar ‘Yancin Jarida ta Duniya na shekarar 2025, wanda aka gudanar a otal ɗin Sheraton da ke Abuja a ranar Juma’a, ƙarƙashin jagorancin Konrad Adenauer Stiftung (KAS) da Cibiyar Ƙirƙire-Ƙirƙiren Jarida da Cigaba (CJID).

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Bukaci Matasa Da Su Ba Da Gudummawar Cimma Nasarar Zamanantar Da Kasa
  • Babu Dalilin Da Zai Sanya Wasu Mambobin PDP Ficewa A Jam’iyyar A Bauchi

Taken taron shi ne: “Rahoto a Sabuwar Duniya – Tasirin AI Kan ‘Yancin Jarida da Kafafen Yaɗa Labarai,” inda aka tattauna yadda Ƙirƙirar Basira take sauya salon aikin jarida da ƙalubalen da ke tattare da hakan.

 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

A cikin jawabin sa a taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wasu manyan fa’idoji da kuma irin barazanar da ke tattare wajen amfani da AI a cikin ɗakunan buga labarai.

 

Ya ce duk da cewa AI na taimaka wa ‘yan jarida a Nijeriya wajen saurin bayar da rahoto, da nazarin bayanai da gudanar da bincike, yana da matuƙar muhimmanci a yi amfani da wannan sabuwar fasahar cikin hankali da bin ƙa’idoji.

 

Ya ce: “A yayin da muke rungumar aikin jarida da fasahar AI, dole ne mu tabbatar da cewa ba za a tauye ‘yancin jarida ba, illa ma a ƙara ƙarfafa shi.”

 

Ministan ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta kafa Cibiyar Ilimin Kafafen Watsa Labarai ta UNESCO a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN), inda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya riga ya amince da kuɗin kafa cibiyar.

 

Ana sa ran wannan cibiyar za ta kasance cibiyar ƙasa da ƙasa da za ta inganta aikace-aikacen kafafen watsa labarai cikin gaskiya da tunani mai zurfi a fannin dijital.

 

Haka kuma, ya bayyana cewa Nijeriya tana kan hanyar ƙaddamar da tsarin dokar ƙasa kan amfani da AI a cikin aikin jarida.

 

Wannan tsari zai ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire amma ba tare da tauye ‘yancin jarida ko karya ƙa’idojin aikin ba.

 

Idris ya buƙaci haɗin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, da masana fasaha, da kafafen yaɗa labarai, da ‘yan siyasa da ƙungiyoyin farar hula domin samar da ƙa’idojin amfani da AI, da koyar da sababbin dabaru, da tabbatar da gaskiya, da kuma faɗakar da al’umma.

 

A nata jawabin, Marija Peran, wakiliyar KAS a Nijeriya, ta jaddada irin damar da AI ke bayarwa ga aikin jarida, tare da yin kashedi kan haɗurran da ke tattare da hakan.

 

Ta ce: “Yana da muhimmanci mu kare ‘yancin kafafen yaɗa labarai a duk duniya, musamman yanzu da AI ke ƙara shiga aikin jarida.

 

“A matsayin ta na ƙungiya mai kishin dimokiraɗiyya da doka da oda, KAS tana tare da kafafen yaɗa labarai wajen fuskantar wannan sabon yanayi.”

 

Taron ya samu halartar mutane daban-daban, ciki har da Shugaban Kwamitin Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Majalisar Wakilai, Honarable Akintunde Rotimi Jr.; da wakilan kafafen yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.