Gwamnatin tarayya ta bayyana Alhamis, 12 ga Yuni, 2025, a matsayin ranar hutu domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta bana.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan, inda ya taya ‘yan Nijeriya murnar cika shekaru 26 na mulkin farar hula ba tare da katsewa ba.
- An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
- Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Wannan sanarwa na ƙunshe ne cikin wata takarda da sakatariyar dindindin ta ma’aikatar harkokin cikin gida, Magdalene Ajani, ta fitar a yau Lahadi.
Tunji-Ojo ya ce: “Ranar 12 ga Yuni tana a matsayin tarihi na ƙoƙarinmu na gina ƙasa inda gaskiya da adalci ke mulki, zaman lafiya ke tabbata kuma makomarmu ke da tabbaci.”
Ya ƙara da cewa dimokuraɗiyya na buƙatar ci gaba da ƙarfafa gwuiwa da sabbin dabaru. Ya jaddada ƙudurin gwamnatin sabon fata (Renewed Hope) ta Shugaba Bola Tinubu wajen kiyaye ƙimomin dimokuraɗiyya da suka ginu kan zabin jama’a wajen tsara tsarin siyasa, tattalin arziki, zamantakewa da al’adu na ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp