• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

by Sadiq
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya (SEC), ta fara binciken wasu kamfanoni 79 da ake zargi da damfarar mutane ta hanyar alƙawarin ninka musu kuɗin da suka zuba.

Wannan nau’in damfara ana kiransa da suna Ponzi scheme.

  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
  • Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

SEC ta ce tana ƙoƙarin wayar da kan jama’a a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar kasuwanni da masallatai domin hana mutane faɗawa cikin tarkon masu yaudarar jama’a.

Duk da haka, masana a fannin tsaron intanet sun ce har yanzu gwamnati tana buƙatar ƙara ƙaimi domin mutane da dama har yanzu suna faɗawa cikin irin waɗannan damfara.

Ɗaya daga cikin kamfanonin da ake bincika shi ne FF Tiffany, wanda ake zargin ya yaudari dubban mutane a Nijeriya da ƙasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hukumar SEC ta ce za ta bayyana sakamakon binciken da ta ke yi a nan gaba.

SEC, ta bayyana irin wannan damfara a matsayin barazana ga amincewar jama’a da harkar zuba jari a ƙasar.

Wannan zai iya hana masu kuɗi yadda su zuba jari.

Dakta Nasir Baba Ahmed, masani a harkar tsaron intanet, ya ce akwai wasu alamu da mutane za su iya lura da su domin gane irin waɗannan damfara.

Hukumar SEC ta ce ta himmatu wajen daƙile duk wani shirin damfara a Nijeriya, kuma tana buƙatar jama’a su bincika shafinta na intanet kafin su zuba kuɗi a kowane kamfani.

Haka kuma, hukumar ta ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan wata doka da za a hukunta duk wanda aka kama da irin wannan damfara da tarar Naira miliyan 20 ko kuma zaman gidan yari na shekara 10.

Dakta Nasir, ya ce dole gwamnati ta aiwatar da wannan doka da kyau, tare da ɗaukar wasu ƙarin matakai domin daƙile wannan matsala gaba ɗaya.

A watan Afrilu na wannan shekara ma, mutane da dama sun yi asarar kuɗi a wani tsarin zuba jari da ake kira CryptoBank Exchange (CBEX) inda aka ce an yi asarar aƙalla Naira tiriliyan ɗaya.

Ko da yake hukumomi sun fara bincike, har yanzu sun ce da wuya a iya dawo da kuɗin jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DamfaraIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Next Post

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Related

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

9 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

1 day ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

1 day ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

2 days ago
Next Post
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.