• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

by Sadiq
5 hours ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya (SEC), ta fara binciken wasu kamfanoni 79 da ake zargi da damfarar mutane ta hanyar alƙawarin ninka musu kuɗin da suka zuba.

Wannan nau’in damfara ana kiransa da suna Ponzi scheme.

  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
  • Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

SEC ta ce tana ƙoƙarin wayar da kan jama’a a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar kasuwanni da masallatai domin hana mutane faɗawa cikin tarkon masu yaudarar jama’a.

Duk da haka, masana a fannin tsaron intanet sun ce har yanzu gwamnati tana buƙatar ƙara ƙaimi domin mutane da dama har yanzu suna faɗawa cikin irin waɗannan damfara.

Ɗaya daga cikin kamfanonin da ake bincika shi ne FF Tiffany, wanda ake zargin ya yaudari dubban mutane a Nijeriya da ƙasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Hukumar SEC ta ce za ta bayyana sakamakon binciken da ta ke yi a nan gaba.

SEC, ta bayyana irin wannan damfara a matsayin barazana ga amincewar jama’a da harkar zuba jari a ƙasar.

Wannan zai iya hana masu kuɗi yadda su zuba jari.

Dakta Nasir Baba Ahmed, masani a harkar tsaron intanet, ya ce akwai wasu alamu da mutane za su iya lura da su domin gane irin waɗannan damfara.

Hukumar SEC ta ce ta himmatu wajen daƙile duk wani shirin damfara a Nijeriya, kuma tana buƙatar jama’a su bincika shafinta na intanet kafin su zuba kuɗi a kowane kamfani.

Haka kuma, hukumar ta ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan wata doka da za a hukunta duk wanda aka kama da irin wannan damfara da tarar Naira miliyan 20 ko kuma zaman gidan yari na shekara 10.

Dakta Nasir, ya ce dole gwamnati ta aiwatar da wannan doka da kyau, tare da ɗaukar wasu ƙarin matakai domin daƙile wannan matsala gaba ɗaya.

A watan Afrilu na wannan shekara ma, mutane da dama sun yi asarar kuɗi a wani tsarin zuba jari da ake kira CryptoBank Exchange (CBEX) inda aka ce an yi asarar aƙalla Naira tiriliyan ɗaya.

Ko da yake hukumomi sun fara bincike, har yanzu sun ce da wuya a iya dawo da kuɗin jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DamfaraIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Next Post

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Related

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

2 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

7 hours ago
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

8 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

23 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Manyan Labarai

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

1 day ago
Next Post
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.