ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

by Sadiq
11 months ago
Intanet

Hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya (SEC), ta fara binciken wasu kamfanoni 79 da ake zargi da damfarar mutane ta hanyar alƙawarin ninka musu kuɗin da suka zuba.

Wannan nau’in damfara ana kiransa da suna Ponzi scheme.

  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
  • Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

SEC ta ce tana ƙoƙarin wayar da kan jama’a a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar kasuwanni da masallatai domin hana mutane faɗawa cikin tarkon masu yaudarar jama’a.

ADVERTISEMENT

Duk da haka, masana a fannin tsaron intanet sun ce har yanzu gwamnati tana buƙatar ƙara ƙaimi domin mutane da dama har yanzu suna faɗawa cikin irin waɗannan damfara.

Ɗaya daga cikin kamfanonin da ake bincika shi ne FF Tiffany, wanda ake zargin ya yaudari dubban mutane a Nijeriya da ƙasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

Hukumar SEC ta ce za ta bayyana sakamakon binciken da ta ke yi a nan gaba.

SEC, ta bayyana irin wannan damfara a matsayin barazana ga amincewar jama’a da harkar zuba jari a ƙasar.

Wannan zai iya hana masu kuɗi yadda su zuba jari.

Dakta Nasir Baba Ahmed, masani a harkar tsaron intanet, ya ce akwai wasu alamu da mutane za su iya lura da su domin gane irin waɗannan damfara.

Hukumar SEC ta ce ta himmatu wajen daƙile duk wani shirin damfara a Nijeriya, kuma tana buƙatar jama’a su bincika shafinta na intanet kafin su zuba kuɗi a kowane kamfani.

Haka kuma, hukumar ta ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan wata doka da za a hukunta duk wanda aka kama da irin wannan damfara da tarar Naira miliyan 20 ko kuma zaman gidan yari na shekara 10.

Dakta Nasir, ya ce dole gwamnati ta aiwatar da wannan doka da kyau, tare da ɗaukar wasu ƙarin matakai domin daƙile wannan matsala gaba ɗaya.

A watan Afrilu na wannan shekara ma, mutane da dama sun yi asarar kuɗi a wani tsarin zuba jari da ake kira CryptoBank Exchange (CBEX) inda aka ce an yi asarar aƙalla Naira tiriliyan ɗaya.

Ko da yake hukumomi sun fara bincike, har yanzu sun ce da wuya a iya dawo da kuɗin jama’a.

MASU ALAKA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.