ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

by Sadiq
1 year ago
Intanet

Hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya (SEC), ta fara binciken wasu kamfanoni 79 da ake zargi da damfarar mutane ta hanyar alƙawarin ninka musu kuɗin da suka zuba.

Wannan nau’in damfara ana kiransa da suna Ponzi scheme.

  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
  • Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

SEC ta ce tana ƙoƙarin wayar da kan jama’a a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar kasuwanni da masallatai domin hana mutane faɗawa cikin tarkon masu yaudarar jama’a.

ADVERTISEMENT

Duk da haka, masana a fannin tsaron intanet sun ce har yanzu gwamnati tana buƙatar ƙara ƙaimi domin mutane da dama har yanzu suna faɗawa cikin irin waɗannan damfara.

Ɗaya daga cikin kamfanonin da ake bincika shi ne FF Tiffany, wanda ake zargin ya yaudari dubban mutane a Nijeriya da ƙasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

Hukumar SEC ta ce za ta bayyana sakamakon binciken da ta ke yi a nan gaba.

SEC, ta bayyana irin wannan damfara a matsayin barazana ga amincewar jama’a da harkar zuba jari a ƙasar.

Wannan zai iya hana masu kuɗi yadda su zuba jari.

Dakta Nasir Baba Ahmed, masani a harkar tsaron intanet, ya ce akwai wasu alamu da mutane za su iya lura da su domin gane irin waɗannan damfara.

Hukumar SEC ta ce ta himmatu wajen daƙile duk wani shirin damfara a Nijeriya, kuma tana buƙatar jama’a su bincika shafinta na intanet kafin su zuba kuɗi a kowane kamfani.

Haka kuma, hukumar ta ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan wata doka da za a hukunta duk wanda aka kama da irin wannan damfara da tarar Naira miliyan 20 ko kuma zaman gidan yari na shekara 10.

Dakta Nasir, ya ce dole gwamnati ta aiwatar da wannan doka da kyau, tare da ɗaukar wasu ƙarin matakai domin daƙile wannan matsala gaba ɗaya.

A watan Afrilu na wannan shekara ma, mutane da dama sun yi asarar kuɗi a wani tsarin zuba jari da ake kira CryptoBank Exchange (CBEX) inda aka ce an yi asarar aƙalla Naira tiriliyan ɗaya.

Ko da yake hukumomi sun fara bincike, har yanzu sun ce da wuya a iya dawo da kuɗin jama’a.

MASU ALAKA

nema
Manyan Labarai

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
ICPC
Manyan Labarai

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
Manyan Labarai

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026
nema

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
Hadarin Kwale-Kwale

Mutum Ɗaya Ya Mutu, Sama Da 30 Sun Ɓace A Hatsarin Kwale-kwale A Jigawa

July 21, 2026
ICPC

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.