Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda aka dakatar daga wakiltar Kogi ta Tsakiya, a gaban kotu a Abuja bisa zargin yin ƙarya da ɓatanci.
An gurfanar da ita a gaban Mai Shari’a Chizoba Orji a Babban Kotun Babban Birnin Tarayya.
- Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
- Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Gwamnatin ta shigar da ƙara kan tuhume-tuhume guda uku da suka shafi zargin ɓata sunan Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello.
An ce zargin ya samo asali ne daga wasu kalamai da ake zargin Sanata Natasha ta faɗa a bainar jama’a, inda ta yi iƙirarin cewa waɗannan manyan ’yan siyasa biyu sun haɗa baki don kashe ta.
Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen, an zarge ta da cewa a wata hira da aka yi da ita a gidan talabijin, ta ce: “Yana cikin abin da suka tattauna a taron da Akpabio ya yi da Yahaya Bello a wancan dare, batun kawar da ni.”
Haka kuma, an ce ta ƙara da cewa: “Mu tambayi Shugaban Majalisar Dattawa, me ya sa ya janye jami’an tsarona tun farko, idan ba don ya sa a kai min hari ba? Ya ce a kashe ni, amma a kashe ni a Kogi.”
Gwamnati ta bayyana cewa waɗannan kalaman suna da nufin ɓata suna, kuma hakan ya saɓa da Sashe na 391 na Dokar Laifuka 89, Dokokin Tarayya na shekarar 1990.
Hukuncin laifin yana ƙarƙashin Sashe na 392 na wannan doka.
A wani tuhumar daban, an zargi Sanata Natasha da yin irin waɗannan kalaman game da Akpabio a cikin wata tattaunawa ta waya da wata Sandra C. Duru a Abuja, a ranar 27 ga watan Maris, 2025.
An ƙara tsaurara tsaro a wajen kotun, inda magoya bayanta da dama suka hallara don nuna goyon baya gare ta.
Daga cikin waɗanda suka halarta akwai mijinta, Emmanuel Uduaghan; tsohuwar Ministar Ilimi, Dokta Oby Ezekwesili; da mashahuriyar mai rajin kare haƙƙin ɗan adam, Aisha Yesufu.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da tsohon Gwamna Yahaya Bello, na cikin jerin shaidu da za a kira a shari’ar.
Sanata Natasha ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba game da tuhumar a yanzu.
An ɗage sauraron ƙarar zuwa wata rana da ba a bayyana ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp