Gwamnatin tarayya ta karrama Nafisa Abdullah Aminu, ‘yar shekara 17, daliba daga jihar Yobe, wacce ta zama ta daya a duniya a gasar ‘TeenEagle’ ta shekarar 2025 da aka gudanar a birnin Landan na kasar Birtaniya.
A wani bikin karramawa na musamman da aka yi a Abuja ranar Alhamis, Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, tare da Karamar Ministar Ilimi, Farfesa Suiwaba Sa’id Ahmad ne suka shirya bikin bajintar da Nafisa ta yi da sauran daliban da suka yi fice a gasar.
- Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru
- Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Sun bayyana ta a matsayin “wata fitacciyar tauraruwa wacce ta zama mai zaburarwa ga matasan Nijeriya.”
Nafisa wacce ta wakilci Nijeriya a karkashin Kwalejin Tulip International ta Nijeriya, ta buge abokan karawarta fiye da 20,000 daga kasashe 69, ciki har da kasashen Turanci.
Gasar ‘TeenEagle’ babbar gasa ce ta duniya wacce ke bibiyar ƙwarewar ɗalibai cikin harshen Turanci, kaifin basira, da ƙwarewa a salon magana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp