• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar Ɗa’a Ta Ƙasa, inji Minista 

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar Ɗa’a Ta Ƙasa, inji Minista 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta fara himmar ƙaddamar da shirin nan na Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa, da nufin bunƙasa ɗabi’u, ɗa’a da kuma farfaɗo da al’adu a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron bita wanda Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) ta gudanar a Abuja a ranar Laraba.

  • Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Dage Da Addu’o’i 
  • Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

A wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, ya raba wa manema labarai, Idris ya bayyana cewa ma’aikatar sa, ta hanyar NOA, ta tsara wannan gagarumin shirin ne domin dukkan ‘yan Nijeriya su samu cikakkiyar fahimta dangane da haƙƙoƙin su a ƙarƙashin tsarin mulkin ƙasa da kuma dokokin ƙasa, sannan su ma gwamnatoci a kowane mataki su san dukkan haƙƙoƙin al’umma da suka rataya a wuyan su kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

 

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

“A ɓangare ɗaya, domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya su san ‘yancin su da kariyar da suke da ita a ƙarƙashin tsarin mulki da dokokin ƙasa sannan kuma gwamnatoci a kowane mataki su san duk wani nauyi na jama’a da kundin tsarin mulki ya ɗora masu. Wannan burin na farko an rubuta shi a cikin ‘Manyan Alƙawurra ‘ bakwai na Yarjejeniyar.

 

“A ɗaya ɓangaren kuma, a wayar da kan dukkan ‘yan Nijeriya kan dukkan nauyin da ya rataya a wuyan mu a matsayin mu na ‘yan wannan ƙasa mai girma da kyau – wanda ke nufin nauyin da ya rataya a wuyan mu ba kawai ga junan mu ba ne, har ma ga gwamnati da ƙasa. Wannan burin na biyu an rubuta shi a cikin ‘Muhimman Alƙawurra’ bakwai na Yarjejeniyar.”

 

Idris ya sha alwashin ci gaba da aiki gadan-gadan babu kama hannun yaro da nufin ganin an samar da ƙasa inda ‘yan ƙasa da ‘ya’yan ta suke ƙaunar juna da girmama juna.

 

Ministan ya ce NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi masu tasiri wajen sauya tunanin jama’ar ƙasa, kawo haɗin kai a ƙasar mai jama’a daban-daban, tare da kawo jituwa da natsuwa a kowane sashe na ƙasar.

 

Ya ce, “Na yi murna da ganin cewa NOA a ƙarƙashin jagorancin Mista Issa-Onilu, ta ba da muhimmanci ga fasahar zamani a aikin hukumar, tana tafiya tare da halin da ake ciki a ƙarni na 21.

 

“NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi waɗanda suka fi yin aiki da fasahar zamani a Nijeriya a yau, suna kan gaba wajen amfani da kayan aiki na fasahar zamani kamar su manhajar The Mobiliser da kuma Fasahar Komfuta (AI) da kowa ya karɓa wajen ƙara wayar da kan jama’a.

 

Idris ya bayyana wannan babban taron bitar a matsayin wani muhimmin mataki da ya dace, wanda aka yi hangen nesa domin samar da wata dama wajen inganta tare da ƙara wa hukumar NOA ƙaimi da nufin tsara kyakkyawar makomar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Dage Da Addu’o’i 

Next Post

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

7 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

10 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

11 hours ago
Next Post
Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.