ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar Ɗa’a Ta Ƙasa, inji Minista 

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Gwamnatin Tarayya ta fara himmar ƙaddamar da shirin nan na Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa, da nufin bunƙasa ɗabi’u, ɗa’a da kuma farfaɗo da al’adu a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron bita wanda Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) ta gudanar a Abuja a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Dage Da Addu’o’i 
  • Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

A wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, ya raba wa manema labarai, Idris ya bayyana cewa ma’aikatar sa, ta hanyar NOA, ta tsara wannan gagarumin shirin ne domin dukkan ‘yan Nijeriya su samu cikakkiyar fahimta dangane da haƙƙoƙin su a ƙarƙashin tsarin mulkin ƙasa da kuma dokokin ƙasa, sannan su ma gwamnatoci a kowane mataki su san dukkan haƙƙoƙin al’umma da suka rataya a wuyan su kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

“A ɓangare ɗaya, domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya su san ‘yancin su da kariyar da suke da ita a ƙarƙashin tsarin mulki da dokokin ƙasa sannan kuma gwamnatoci a kowane mataki su san duk wani nauyi na jama’a da kundin tsarin mulki ya ɗora masu. Wannan burin na farko an rubuta shi a cikin ‘Manyan Alƙawurra ‘ bakwai na Yarjejeniyar.

 

“A ɗaya ɓangaren kuma, a wayar da kan dukkan ‘yan Nijeriya kan dukkan nauyin da ya rataya a wuyan mu a matsayin mu na ‘yan wannan ƙasa mai girma da kyau – wanda ke nufin nauyin da ya rataya a wuyan mu ba kawai ga junan mu ba ne, har ma ga gwamnati da ƙasa. Wannan burin na biyu an rubuta shi a cikin ‘Muhimman Alƙawurra’ bakwai na Yarjejeniyar.”

 

Idris ya sha alwashin ci gaba da aiki gadan-gadan babu kama hannun yaro da nufin ganin an samar da ƙasa inda ‘yan ƙasa da ‘ya’yan ta suke ƙaunar juna da girmama juna.

 

Ministan ya ce NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi masu tasiri wajen sauya tunanin jama’ar ƙasa, kawo haɗin kai a ƙasar mai jama’a daban-daban, tare da kawo jituwa da natsuwa a kowane sashe na ƙasar.

 

Ya ce, “Na yi murna da ganin cewa NOA a ƙarƙashin jagorancin Mista Issa-Onilu, ta ba da muhimmanci ga fasahar zamani a aikin hukumar, tana tafiya tare da halin da ake ciki a ƙarni na 21.

 

“NOA ta zama ɗaya daga cikin hukumomi waɗanda suka fi yin aiki da fasahar zamani a Nijeriya a yau, suna kan gaba wajen amfani da kayan aiki na fasahar zamani kamar su manhajar The Mobiliser da kuma Fasahar Komfuta (AI) da kowa ya karɓa wajen ƙara wayar da kan jama’a.

 

Idris ya bayyana wannan babban taron bitar a matsayin wani muhimmin mataki da ya dace, wanda aka yi hangen nesa domin samar da wata dama wajen inganta tare da ƙara wa hukumar NOA ƙaimi da nufin tsara kyakkyawar makomar Nijeriya.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.