ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

by Leadership Hausa
2 years ago
Ta'adda

Kisan da aka yi wa Alhaji Isa Muhammad Bawa, Sarkin Gobir na Gatawa da ke Jihar Sakkwato kwanannan ya kara fito da tsanannin matsalar tsaro a Nijeriya. Lamarin da ya faru a ranar 21 ga watan Agusta 2024 ya tayar da hankali matuka a kan tsaron lafiyar Sarakunan gargajiya a Nijeriya da ma sauran ‘yan Nijeriya gaba daya ya kuma fito da iri hali da iya aiki ko akasinsa na jami’an tsaron mu.

Kasancewar Sarkin Gobir Bawa da dansa sun kasannce a hannu ‘yan ta’adda na kusan wata daya kafin su kashe shi, duk kuwa da kokarin ceto shi da aka yi ya nuna sakaci da rashin iya aiki na masu tafiyar da harkokin tsaron kasar nan a wannan irin halin tabarbarewar tsaron da ake ciki.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

An kama Sarkin Gobir Bawa ne a ranar 27 ga watan Yuli,2024, tare da dansa, Kabiru Isa, yayin da suke dawowa daga taro a fadar Sarkin Musulmi da aka yi Sakkwato. Duk kokarin da iyalansa da masarautar Gobir ta yi ga gwamatin Jihar har ma da sakon bidiyon da aka turo daga mabuyar ‘yan ta’adda hakan bai wani taimaka ba. Lokacin da aka kai kudin fansa na naira Miliyan 60 da ‘yan ta’addan suka nema lokaci ya kure domin sun dade da kashe shi inda daga baya suka sako dansa.

ADVERTISEMENT

Bayan mutuwarsa, kamar dai kowane lokaci sai ihun tir da kisan ke fitowa daga dukkan bangarori, inda gwamati ta sha alwashin kamo wadanda suka yi kisan. Wannan bai isa ba domi tamkar shan magani ne bayan mutuwa ne, ya kamata a ce jamai’an tsaro sun bi sawun masu garkuwa kamar yadda suka bi sawun wadanda suka sace dalibai likitoci na jami’ar Benuwai.Muna jinjina ga kokarin al’umma yankin maza da mata da suka fatattaki ‘yan ta’adda inda suka kwato gawar marigayi Sarkin suka kuma kwato wasu da aka yi garkuwa da su. Wannan abin da ya faru da a wasu kasashe ne da lallai an hukunta wasu daga cikin jami’an tsaron da ke da alhakin tabbatar da tsaro a yankin.

A watan Mayun 2024, ‘yan bindiga sun kashe Chif Auwal Wali, Sarkin gargajiya na Gidan Usmanu da ke Jihar Taraba.Hakanan kuma a watan Yuli ‘yan bindiga sun yi wa Sarkin Takum, Tanimu Kunbiya da dansa kwantan bauna yayin da suke dawowa daga wata jana’iza a jihar Taraba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

A watan Agusta 2024, Sarakunan gargajiya da Sarakunan kauyuka 6 a garin Umucheke Okwe da ke karamar hukumar Onuimo na Jihar Imo aka kashe yayin da suke gudanar da wani taron neman zaman lafiya. Haka kuma a watan Yuli na shekarar data gabata an kashe sarakunan gargajiya da dama ciki har da na Nguru da ke karamar hukumar Aboh Mbaise,Eze Mmirioma, da Eze Joe-Benz Ochulor, Olu 1 na Otulu Amumara na masarautar Ezinihitte Mbaise da ke Jihar Imo.

A farkon watan Agusta, ‘yan bindiga sun kashe basaraken Umuihe da ke Jihar Ebonyi State, mai martaba Umazi Ibo Ubani.

A watan Disamba na shekarar 2023, ‘yan ta’adda sun kashe hakimin Yankuzo, Alhaji Hamza Kogo, da ke masarautar Tsafe a Jihar Zamfara a lokacin da suka yi kokarin yin garkuwa da shi da iyalansa.Haka kuma a shekarar 2020 aka kashe basaraken Olufon na Ifon, Oba Israel Adeusi, a kan babbar hanyar Ifonzuwa Benin a daidai watan Nuwamba na shekarar 2020.An dade ana aikata ta’addanci a kan Sarakunan gargajiya, rahotannin sun nuna cewa, an kashe fiye da sarakuna gargajiya 53 a cikn shekara 10 da suka wuce, kamar dai yadda rahoton wata kungiya mai zaman kanta mai suna SMB 2021 ta ruwaito.

Ya kamata a kawo karshen ta’addanci a kan Sarakunan gargajiya.Dole ne gwamati da jami’an tsaro su samar da yanayi na tsaro ga Sarakunan gargajiya da ‘yan kasa baki daya. Wannan kuma ba yana nufin samar masu jami’an tsaro masu kare lafiyarsu kadai ba, harma da samar da hanyoyin tattara bayanan sirri domin katse kokari da shirin ‘yan ta’adda na kai hari da sace Sarakunan gargajiya a sassan Nijeriya.

Karfafa hanyoyin tsaro a tsakanin al’umma zai taimaka wajen tabbatar da tsaro da kuma kawo karshen harkokin ‘yan ta’adda da ta’addanci a kasa, zai kuma taimaka wajen kawo karshen yadda ake sace Sarakunan gargajiya a kasar nan.

Wani rahoto da bincikenh da aka gudanar kwanan nan ya nuna yadda aka biya fiye da naira biliyan 1 a matsayin kudin fansa a tsakanin watan Yuli na shekarar 2023 zuwa watan Yuni na shekara 2024. Wadannan kudin hana shigewa ne ta hanyar bankuna. Ya kamata ayi amfani da hanyoyi na zamani wajen bin sawun kudaden tare da kama ‘yan ta’addar da masu daukar nauyinsu.

Ya kuma kamata Nijeriya ta hada kai da kwararru daga kasashen waje wajen yaki da harkokin ta’addanci da ‘yan ta’adda musamman ma ganin matsalolin tsaron da ake fuskanta a kasar nan suna da yawan gaske.

Kisan Sarkin Gobir Bawa da yadda ayyukan ta’addanci ke kara karuwa yana nuna raunin masu tafiyar da harkokin gwamanti a kasar nan.

A yayin da muke alhinin kashe-kashen da ake yi mana, ya kamata mu hada karfi da karfe wajen kawo karshen ayyukan ‘yan ta’adda da ta’addanci a sassan kasar nan musamman ma yadda ake ci wa Sarakunan gargajiyar mutunci wadanda sune ke dauke da mutuncin mu da al’adun mu.

Ta'adda
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.