• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Abinci 4,200 Ga Marasa Karfi A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta raba kayayyakin abinci da yawansu ya kai buhu dubu hudu da dari biyu (4,200) ga al’ummar jihar Bauchi domin rage kaifin talauci da fatara a tsakanin al’umma.

Kayan abincin sun kunshi buhun Dawa 1,200, buhun Masara 1,200, buhunan Garin Kwaki 1,200 da kuma Gero buhu 600 domin raba wa marasa karfi a cikin al’umman jihar.
Da take mika kayayyakin a sakatariyar APC da ke Bauchi, karamar ministan ma’aikatar kasuwanci da masana’antu da zuba hannun jari, Ambasada Mariam Yalwaji Katagum, ta ce, tallafin an yi ne domin rage wa mutanen da suke fama da wahalar rayuwa dawainiyar da suke ciki.

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 11, Ya Jikkata 8 A Bauchi

Ministar wacce ta samu wakilcin babban mai bada shawara, Dakta Ahmad Mabudi, ta misalta tallafin a matsayin wani bangare na kokarin shugaban kasa Muhammadu Buhari na cire miliyoyin mutane daga kangin talauci da fatara.

“Babbar fatanmu a nan shine a tabbatar an yi adalci wajen rabon, kuma ina jawo hankalin masu kula da rabon da su tabbatar sun yi adalci domin wadanda suka cancanta su samu daga kowace jam’iyya kuma mutum ya fito ba wai zallar ‘yan APC ba.”
Katagum ta jinjina wa jagororin jam’iyyar APC na jihar Bauchi bisa kokarin da suka yi wajen ganin an samu nasarar kawo wannan tallafin.

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC na jihar Bauchi Alhaji Babayo Aliyu Misau, wanda ya samu wakilcin sakataren jam’iyyar, Mustapha Zirami, ya ce, an samar da kayan abincin ne da nufin raba wa ga marasa karfi da suke fadin jihar.

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Ya kuma ce, za a rabar da kayan abincin ne ga kowani bangare ba tare da la’akari daga wacce jam’iyya mutum ya fito ba.
Ya gode wa ministar bisa wannan abinci da ta yi tsayuwar daka wajen kawo shi jihar, sai ya jawo hankalin masu alhalin rabon da su ji tsoron Allah kada su sanya son zuciya wajen yin rabon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Cutar Da Ta Barke A Sansanin ‘Yan Gudun Hijiranmu – Gwamnatin Kogi

Next Post

Duk ‘Ya’yan Kungiyarmu Ba Su Da Kudin Motar Zuwa Aiki —Shugaban ASUU

Related

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

1 hour ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

2 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

5 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

6 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

7 hours ago
Next Post
Duk ‘Ya’yan Kungiyarmu Ba Su Da Kudin Motar Zuwa Aiki —Shugaban ASUU

Duk 'Ya'yan Kungiyarmu Ba Su Da Kudin Motar Zuwa Aiki —Shugaban ASUU

LABARAI MASU NASABA

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.