• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Samar Da Rumbun Adana Bayanai Don Tallafa Wa Manoma

by Abubakar Abba
10 months ago
Rumbun

Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, ta rattaba hannun yarjejeniya da Hukumar Bayar da Katin Shedar Dan Kasa (NIMC), domin kirkiro da rumbun adana bayanai, don bai wa manoma tallafin aikin noma.

Manufar shirin shi ne, kara habaka fannin aikin noma tare da samar da wadataccen abinci a Nijeriya, hakan kuwa; ya kasance cikin kudurori takwas na Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Rumbun, wanda za a yi masa lakabi da yi wa manoma rijista, za a bukaci amfani da daukar bayanan manoman, domin gano sahihan manoman da za su amfana da tallafin tare kuma da tabbatar da ganin sun mallaki gonaki.

A kashin farko na shirin, ana sa ran yi wa manoma miliyan biyu rijista cikin wata uku, inda kuma za a yi wa kashi na biyu su kimanin miliyan shida rijistar.

A cikin wata uku, Hukumar ta NIMC, za ta iya samun bayanan manoman tare da hada rukuni don cimma burin gudanar da shirin.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Har ila yau, don hukumar ta samu damar isa ga manoman wajen gudanar da shirin, za ta yi hadaka da kamfanoni masu zaman kansu tare kuma yin aiki da sauran ofisoshiinta da ke daukacin kanannan hukumomin wannan kasa.

Shirin ya kuma kunshi amfani da bayar da katin da za a yi amfani da shi, domin cire kudin tallafin noma ga manoman.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Abubakar Kyari, ya bayyan haka ne a jawabinsa wajen taron rattaba hannun wannan yarjejeniyar da aka gudanar a shalkwatar ma’aiktar, ranar Laraba a babban birnin tarayya Abuja.

“Abin da muka rattaba hannun a halin yanzu da hukumar kasa da kasa shi ne, bunkasa yi wa manoma rijista”, in ji Kyari.

Kazalika, ya kara da cewa; za mu yi amfani da manhajar rumbun adana bayanai na Hukumar NIMC, domin samar da katin shedar dan kasa (NIN), tare kuma da sama wa manoman katin da zai dauki bayanansu.

“Da farko dai, za mu gano gonakin da manoman suka mallaka tare da yin nomansu, wanda hakan zai ba mu damar sanin gonakin da suke nomawa, domin yi su rijistar”, a cewar Kyari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.