• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Sayar Da Kamfanonin Samar Da Wuta 4

by Bello Hamza
2 years ago
TCN

A halin yanzu gwamnatin tarayya da bayar da umarnin sake sayar da wasu kamfanonin samar da wutar lantarki 4 ta kuma umarci a sake rarraba wasu kamfanonin zuwa kananan kamfanoni saboda girmansu ya na kawo cikas ga yadda suke gudanar da ayyukansu.

Sanarwar ta kuma ce gwamnati ba za ta janye sayar da kamfanonin da ta yi ba amma za a sake rarraba su don su samu yin aiki yadda ya kamata, al’umma su amfana da ayyukansu ba kamar yadda lamarin yake a halin yanzu ba.

  • Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani
  • Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo

Wannan kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin a sayar da wasu kamfanoni samar da wutar lantarki 4 (Discos) wadanda bankuna da kamfanin AMCON suka karbe ragamar tafiyar da su saboda basuka.

Bankin UBA ne ta karbe harkokin kamfanin samar da wuta na Abuja yayin da bankin Fidelity Bank ya karbe harkokin kamfanin samar da wuta na Benin da Kaduna da na Kano. Sai kuma kamfanin samar da wuta na Ibadan da ya koma karkashin kamfanin AMCON. An yanke wa wadannan kamfannnin hukuncin ne saboda sun kasa biyan kudaden da wadannan bankuna ke binsu.

Gwamnati ta bayyana cewa, wadanda suka sayi kamfanonin a lokacin da aka yi gwanjon su ne tunda farko a shekarar 2013 ne basu da kudi da kuma kwarewar da ake bukata na tafiyar da kamfanoni irin wannan.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Wannan ma yana zuwa ne a yayin da majalisar dattawa ta caccaki kamfanonin Discos a kan rashin iya aiki tun da aka sayar musu da kamfanonin a shekara 10 da suka wuce.

A jawabinsa a yayin da ‘yan kwamitin majalisar dattawa a kan wutar lantarki a karkashin jagorancin Sanata Eyinnaya Abaribe, suka kai masa ziyara, Ministan wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa, a halin yanzu gwamnatin tarayya ta fara aikin sake fasalin kamfanonin samar da wuta 11 na kasar nan.

Ya ce, akwai ayyyuka fiye da 100 da kamfanonin suka bayar amma fiye da shekara 23 da suka wuce amma har yanzu ba a kammala ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Fashewar Bututun Iskar Gas Na Nord Stream Karkashin Jagorancin MDD

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Fashewar Bututun Iskar Gas Na Nord Stream Karkashin Jagorancin MDD

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.