• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Albarkatun Teku, Adegboyega Oyetola, ya bayyana cewa, akwai bukatar a gaggauta farfado tare dda bunkasa kayayyakin aiki da ke tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island da ke Ledgas, ya kuma yaba da yadda Shugaban Tashoshin Ruwan Nijeriya NPA Muhammed Bello Koko yake gudanar da ayyukansa.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da kai ziyarar gani da ido a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island a karkashin jagorancin shugaban Tashoshin Jiraghen Ruwan Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, a Legas, Ministan ya kara da cewa, domin kaucewa tsayawar harkokin gudanawar tashoshin ya zama dole a gaggauta farfado da kayyakin da ke tashar don su ci gaba da aiki yadda ya kamata a kan haka ya nemi masu gudanar da ayyuka a tashar su tabbatar da ba hukumar NPA da gwamnatin tarayya goyon baya don a cimma wannan gaggarumin aiki na sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Legas.

  • Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF
  • Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah S.A.W (2)

Ministan ya kuma kara jadda cewa, “Domin kaucewa durkushewar ayyuka a tashar jiragen ruwan dole mu gaggauta sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tincan Island sannan kuma ya kamata a ci gaba da shirin yashe tekun don ayyuka su ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

“Na zagaya na kuma ga abubuwa da kaina, na yi taro da tattauanawa a cikin kwanaki 10 da suka wuce na kuma fahimci abubuwa da dama a kan haka nake kara jadda bukatar sabunta tare da bunkasa kayan aiki a tashoshin jiragen ruwanmu gaba daya.

“Kayayyakin duk sun nemi durkushewa, abin  da na gani da ido na lallai ya kamata a sabunta kayayyakin tare da ci gaba da yashe teku.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Tsohon gwamnan jihar Osun ya kuma yaba wa hukumar gudanarwa NPA, ya ce lallai suna bukatar goyon baya don a samu cimma abubuwan da ake bukata.

“Na yaba da yadda hukumar gudanarwar suke tafiyar da harkokinsu. Lallai ya kamata mu goya musu baya, ina kuma fatan masu gudanar da wasu bangarorin tashar za su bayar da nasu goyon bayan wajen farfado da tashar, goyon bayan su na da matukar muhimmanci don ta haka za su kara samun kudin shiga, haka kuma gwamnati za ta kara samun kudaden shiga, wannan lamari na hadin kai a tsakanin gwamanati da dukkan masu harkoki a ciki da wajen tashoshin gaba daya.

“Zamu fara wasu ayyukan gaggawa a tashar jirane ruwan, na bukaci a samar da cikakken rahoton yadda aikin zai gudana don mu san abin da aikin zai ci, don mu san kudaden da za mu nemi izinin kashe daga fadar shugaban kasa.

Tabbas muna da tsananin bukatar farfado da kayayyakin aiki a tashar domin ta haka ne zamu farfado ayyuka a tashar, ta haka ne kuma zamu samu karin kudaden shiga da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya gaba daya. Muna tsananin dogaro ga mai amma kuma gashi a wannan bangaren akwai arziki sosai da ba a taba ba, dole mu mika godiya ga shugaban kasa a bisa yadda ya kirkiro wannan ma’aikatar.”

Ministan ya kuma ce, zai tuntubi ma’aikatar ayyuka don ganin yadda za a gyara hanyar da ta shiga tashar NPA. Daga karshe ya yi jinjina ga ayyuka da kokarin shugaban NPA Muhammed Bello Koko a kan yadda yake tafiyar da harkokin hukumar, ya kuma nemi ya kara kaimi domin akwai gaggarumnin aiki a gaba.

A nasa tsokacin, Shugaban NPA, Mohamed Belllo Koko ya mika godiya ga Ministan da tawagarsa a bisa ziyarar aiki da suka kawo, ya kuma yi alkawarin ci gaba da aiki yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF

Next Post

Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

59 seconds ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

1 hour ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

2 hours ago
Labarai

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

5 hours ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

6 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

8 hours ago
Next Post
Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.