• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Albarkatun Teku, Adegboyega Oyetola, ya bayyana cewa, akwai bukatar a gaggauta farfado tare dda bunkasa kayayyakin aiki da ke tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island da ke Ledgas, ya kuma yaba da yadda Shugaban Tashoshin Ruwan Nijeriya NPA Muhammed Bello Koko yake gudanar da ayyukansa.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da kai ziyarar gani da ido a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island a karkashin jagorancin shugaban Tashoshin Jiraghen Ruwan Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, a Legas, Ministan ya kara da cewa, domin kaucewa tsayawar harkokin gudanawar tashoshin ya zama dole a gaggauta farfado da kayyakin da ke tashar don su ci gaba da aiki yadda ya kamata a kan haka ya nemi masu gudanar da ayyuka a tashar su tabbatar da ba hukumar NPA da gwamnatin tarayya goyon baya don a cimma wannan gaggarumin aiki na sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Legas.

  • Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF
  • Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah S.A.W (2)

Ministan ya kuma kara jadda cewa, “Domin kaucewa durkushewar ayyuka a tashar jiragen ruwan dole mu gaggauta sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tincan Island sannan kuma ya kamata a ci gaba da shirin yashe tekun don ayyuka su ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

“Na zagaya na kuma ga abubuwa da kaina, na yi taro da tattauanawa a cikin kwanaki 10 da suka wuce na kuma fahimci abubuwa da dama a kan haka nake kara jadda bukatar sabunta tare da bunkasa kayan aiki a tashoshin jiragen ruwanmu gaba daya.

“Kayayyakin duk sun nemi durkushewa, abin  da na gani da ido na lallai ya kamata a sabunta kayayyakin tare da ci gaba da yashe teku.”

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Tsohon gwamnan jihar Osun ya kuma yaba wa hukumar gudanarwa NPA, ya ce lallai suna bukatar goyon baya don a samu cimma abubuwan da ake bukata.

“Na yaba da yadda hukumar gudanarwar suke tafiyar da harkokinsu. Lallai ya kamata mu goya musu baya, ina kuma fatan masu gudanar da wasu bangarorin tashar za su bayar da nasu goyon bayan wajen farfado da tashar, goyon bayan su na da matukar muhimmanci don ta haka za su kara samun kudin shiga, haka kuma gwamnati za ta kara samun kudaden shiga, wannan lamari na hadin kai a tsakanin gwamanati da dukkan masu harkoki a ciki da wajen tashoshin gaba daya.

“Zamu fara wasu ayyukan gaggawa a tashar jirane ruwan, na bukaci a samar da cikakken rahoton yadda aikin zai gudana don mu san abin da aikin zai ci, don mu san kudaden da za mu nemi izinin kashe daga fadar shugaban kasa.

Tabbas muna da tsananin bukatar farfado da kayayyakin aiki a tashar domin ta haka ne zamu farfado ayyuka a tashar, ta haka ne kuma zamu samu karin kudaden shiga da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya gaba daya. Muna tsananin dogaro ga mai amma kuma gashi a wannan bangaren akwai arziki sosai da ba a taba ba, dole mu mika godiya ga shugaban kasa a bisa yadda ya kirkiro wannan ma’aikatar.”

Ministan ya kuma ce, zai tuntubi ma’aikatar ayyuka don ganin yadda za a gyara hanyar da ta shiga tashar NPA. Daga karshe ya yi jinjina ga ayyuka da kokarin shugaban NPA Muhammed Bello Koko a kan yadda yake tafiyar da harkokin hukumar, ya kuma nemi ya kara kaimi domin akwai gaggarumnin aiki a gaba.

A nasa tsokacin, Shugaban NPA, Mohamed Belllo Koko ya mika godiya ga Ministan da tawagarsa a bisa ziyarar aiki da suka kawo, ya kuma yi alkawarin ci gaba da aiki yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF

Next Post

Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

7 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

7 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

8 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

9 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

10 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

12 hours ago
Next Post
Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.