ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

by Bello Hamza
3 years ago
Koko

Ministan Albarkatun Teku, Adegboyega Oyetola, ya bayyana cewa, akwai bukatar a gaggauta farfado tare dda bunkasa kayayyakin aiki da ke tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island da ke Ledgas, ya kuma yaba da yadda Shugaban Tashoshin Ruwan Nijeriya NPA Muhammed Bello Koko yake gudanar da ayyukansa.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da kai ziyarar gani da ido a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tin-Can Island a karkashin jagorancin shugaban Tashoshin Jiraghen Ruwan Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, a Legas, Ministan ya kara da cewa, domin kaucewa tsayawar harkokin gudanawar tashoshin ya zama dole a gaggauta farfado da kayyakin da ke tashar don su ci gaba da aiki yadda ya kamata a kan haka ya nemi masu gudanar da ayyuka a tashar su tabbatar da ba hukumar NPA da gwamnatin tarayya goyon baya don a cimma wannan gaggarumin aiki na sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Legas.

  • Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF
  • Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah S.A.W (2)

Ministan ya kuma kara jadda cewa, “Domin kaucewa durkushewar ayyuka a tashar jiragen ruwan dole mu gaggauta sabunta kayan aiki a tashar jiragen ruwa na Apapa da Tincan Island sannan kuma ya kamata a ci gaba da shirin yashe tekun don ayyuka su ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

“Na zagaya na kuma ga abubuwa da kaina, na yi taro da tattauanawa a cikin kwanaki 10 da suka wuce na kuma fahimci abubuwa da dama a kan haka nake kara jadda bukatar sabunta tare da bunkasa kayan aiki a tashoshin jiragen ruwanmu gaba daya.

“Kayayyakin duk sun nemi durkushewa, abin  da na gani da ido na lallai ya kamata a sabunta kayayyakin tare da ci gaba da yashe teku.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsohon gwamnan jihar Osun ya kuma yaba wa hukumar gudanarwa NPA, ya ce lallai suna bukatar goyon baya don a samu cimma abubuwan da ake bukata.

“Na yaba da yadda hukumar gudanarwar suke tafiyar da harkokinsu. Lallai ya kamata mu goya musu baya, ina kuma fatan masu gudanar da wasu bangarorin tashar za su bayar da nasu goyon bayan wajen farfado da tashar, goyon bayan su na da matukar muhimmanci don ta haka za su kara samun kudin shiga, haka kuma gwamnati za ta kara samun kudaden shiga, wannan lamari na hadin kai a tsakanin gwamanati da dukkan masu harkoki a ciki da wajen tashoshin gaba daya.

“Zamu fara wasu ayyukan gaggawa a tashar jirane ruwan, na bukaci a samar da cikakken rahoton yadda aikin zai gudana don mu san abin da aikin zai ci, don mu san kudaden da za mu nemi izinin kashe daga fadar shugaban kasa.

Tabbas muna da tsananin bukatar farfado da kayayyakin aiki a tashar domin ta haka ne zamu farfado ayyuka a tashar, ta haka ne kuma zamu samu karin kudaden shiga da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya gaba daya. Muna tsananin dogaro ga mai amma kuma gashi a wannan bangaren akwai arziki sosai da ba a taba ba, dole mu mika godiya ga shugaban kasa a bisa yadda ya kirkiro wannan ma’aikatar.”

Ministan ya kuma ce, zai tuntubi ma’aikatar ayyuka don ganin yadda za a gyara hanyar da ta shiga tashar NPA. Daga karshe ya yi jinjina ga ayyuka da kokarin shugaban NPA Muhammed Bello Koko a kan yadda yake tafiyar da harkokin hukumar, ya kuma nemi ya kara kaimi domin akwai gaggarumnin aiki a gaba.

A nasa tsokacin, Shugaban NPA, Mohamed Belllo Koko ya mika godiya ga Ministan da tawagarsa a bisa ziyarar aiki da suka kawo, ya kuma yi alkawarin ci gaba da aiki yadda ya kamata.

Koko
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.