ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF

by Bello Hamza
3 years ago
PACF

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

A karshen makon jiya ne gamayyar kungiyar ‘yan kasuwa masu harkokin kasuwanci a fadin yankin nahiyarmu ta Afrika ‘Pan African Competitibeness Forum (PACF)’ ta gudanar da zaben sabbin shugabanni da za su karbi akalar shugabancin kungiyar na wasu shekaru masu zuwa inda cikin ikon Allah aka tabbatar da zabar Dakta Abubakar Tanko Bala a matsayin Babban Sakataren Kungiyar tare da wasu jami’a da za su rike mukamai daban-daban a kungiyar don samar da ci gaba mai dorewa a kungiyar.

Shi dai Dakta Abubakar Tanko Bala dan kasuwa ne kuma kararren masani mai bayar da shawarwarin yadda za a bunkasa harkokin kasuwanci, kuma a halin yanazu yana rike da mukamin ma’ajin kungiyar masu kananan masana’antu na kasa (NASSI).

  • Cikar Gwamnoni Kwana 100 A Karagar Mulki: Me Aka Tabuka A Jigawa, Bauchi, Nasarawa, Gombe, Borno Da Yobe?
  • A Kawo Karshen Barnata Karafunan Hanyar Jiragen Kasa A Nijeriya

Taron da aka yi inda aka zabi Dakta Abubakar Tanko Bala ya gudana ne a babban birnin tarayya Abuja, kamar yadda jami’ar watsa labarai na kungiyar, reshen Nijeriya, Fa’iza Shehu, ta bayyana a takardar manema labarai da ta sawa hannu, ta kuma kara da cewa, babban makasudin kungiyar shi ne samar da yanayin bunkasa harkar kasuwanci da kuma ba kowa damar da yake bukata don samun nasara ba tare da takurawa ba a tsakanin ‘yan kasuwan yankin Afrika gaba daya.

A zaben da aka gudanar, Alhaji Garba Ibrahim Gusau Mni, MFR ya samu nasarar zama shugaban kungiyar ta PACF yayin da Alhaji Abdul-Fatah Shittu ya zama ma’ajin kungiyar na Afrika inda Dakta Abubakar Tanko Bala ya samu nasarar zama babban sakataren kungiyar.

Taron ya samu gaggarumin nasara, ana kuma fatan samun nasarar Dakta Abubakar a matsayin babban sakataren kungiyar zai samar da nasarar bunkasa kungiyar, saboda ganin dimbin kwarewarsa da kuma sanin makaman aikiinsa.

A tattanawarsa da manema labarai bayan an sanar da nasararsa, Dakta Abubakar Tanko ya bayyana cewa, a matsayinsa na babban sakataren kungiyar PACF zai bayar da gudummawarsa ga bunkasar kungiyar tare da tabbatar da Nijeriya ta ci gajiyar kasancewarta a cikin kungiyar ta yadda Nijeriya za ta kasance a gaba a tsakanin kasashen Afrika a fannin kasuwanci, ya kuma mika godiyarsa ga dukkan wadanda suka bashi goyon bayan samun nasara, ya kuma yi alkwarin aiki tare da sauran shugabannin kungiyar don kai kungiyar ga tudun mun tsira, daga karshe ya yi alkawarin aiki da dukkan masu ruwa da tsaki wajen samar wa matasanmu aiki tare da koya musu hanyoyin dogaro da kai.

PACF
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.