ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Dakta Abubakar Tanko Bala Ya Zama Sabon Sakataren Kungiyar PACF

by Bello Hamza
3 years ago
PACF

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A karshen makon jiya ne gamayyar kungiyar ‘yan kasuwa masu harkokin kasuwanci a fadin yankin nahiyarmu ta Afrika ‘Pan African Competitibeness Forum (PACF)’ ta gudanar da zaben sabbin shugabanni da za su karbi akalar shugabancin kungiyar na wasu shekaru masu zuwa inda cikin ikon Allah aka tabbatar da zabar Dakta Abubakar Tanko Bala a matsayin Babban Sakataren Kungiyar tare da wasu jami’a da za su rike mukamai daban-daban a kungiyar don samar da ci gaba mai dorewa a kungiyar.

Shi dai Dakta Abubakar Tanko Bala dan kasuwa ne kuma kararren masani mai bayar da shawarwarin yadda za a bunkasa harkokin kasuwanci, kuma a halin yanazu yana rike da mukamin ma’ajin kungiyar masu kananan masana’antu na kasa (NASSI).

  • Cikar Gwamnoni Kwana 100 A Karagar Mulki: Me Aka Tabuka A Jigawa, Bauchi, Nasarawa, Gombe, Borno Da Yobe?
  • A Kawo Karshen Barnata Karafunan Hanyar Jiragen Kasa A Nijeriya

Taron da aka yi inda aka zabi Dakta Abubakar Tanko Bala ya gudana ne a babban birnin tarayya Abuja, kamar yadda jami’ar watsa labarai na kungiyar, reshen Nijeriya, Fa’iza Shehu, ta bayyana a takardar manema labarai da ta sawa hannu, ta kuma kara da cewa, babban makasudin kungiyar shi ne samar da yanayin bunkasa harkar kasuwanci da kuma ba kowa damar da yake bukata don samun nasara ba tare da takurawa ba a tsakanin ‘yan kasuwan yankin Afrika gaba daya.

A zaben da aka gudanar, Alhaji Garba Ibrahim Gusau Mni, MFR ya samu nasarar zama shugaban kungiyar ta PACF yayin da Alhaji Abdul-Fatah Shittu ya zama ma’ajin kungiyar na Afrika inda Dakta Abubakar Tanko Bala ya samu nasarar zama babban sakataren kungiyar.

Taron ya samu gaggarumin nasara, ana kuma fatan samun nasarar Dakta Abubakar a matsayin babban sakataren kungiyar zai samar da nasarar bunkasa kungiyar, saboda ganin dimbin kwarewarsa da kuma sanin makaman aikiinsa.

A tattanawarsa da manema labarai bayan an sanar da nasararsa, Dakta Abubakar Tanko ya bayyana cewa, a matsayinsa na babban sakataren kungiyar PACF zai bayar da gudummawarsa ga bunkasar kungiyar tare da tabbatar da Nijeriya ta ci gajiyar kasancewarta a cikin kungiyar ta yadda Nijeriya za ta kasance a gaba a tsakanin kasashen Afrika a fannin kasuwanci, ya kuma mika godiyarsa ga dukkan wadanda suka bashi goyon bayan samun nasara, ya kuma yi alkwarin aiki tare da sauran shugabannin kungiyar don kai kungiyar ga tudun mun tsira, daga karshe ya yi alkawarin aiki da dukkan masu ruwa da tsaki wajen samar wa matasanmu aiki tare da koya musu hanyoyin dogaro da kai.

PACF
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.