• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
Kaduna

Biyo bayan harin bam da aka kai kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya za ta sake gina wa mazauna kauyen gidaje, Makaranta da Asibiti sannan kuma za ta samar musu da kayan Noma.

Shi ma, Gwamna Uba Sani ya baiwa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su tallafi, inda ya ce, gwamnati za ta dauki nauyin kudin duk abinda ake bukata wajen jinya ga wadanda suka jikkata kuma ake duba lafiyarsu a asibitin koyarwa na Barau Dikko da ke jihar Kaduna.

  • Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba
  • A Magance Rashin Aikin Yi A Tsakanin Matasa

Bugu da kari, Gwamnan ya sha alwashin bayar da tallafi na kudi, kula da lafiyar kwakwalwa da kayan masarufi ga marayun da suka rasa masu kula da su a wannan mummunan lamari.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya tarbi wata tawagar jiga-jigan gwamnatin tarayya da suka hada da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, kakakin majalisar wakilai Abbas Tajuddeen, ministan tsaro Mohammed Badaru Abubakar, da shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Gwamna Sani ya kuma mika godiyarsa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta mika ta’aziyyarsa kan ibtila’in inda kuma ya bada umurnin gudanar da bincike cikin gaggawa don gano musabbabin kai harin.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

Gwamnan ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, za a bayyanawa Jama’a sakamakon binciken da zarar an kammala, sannan ya jaddada kudirin Shugaba Tinubu na biyan diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da kaddamar da sake gina muhimman ababen more rayuwa a cikin al’ummar Tudun Biri.

Acewarsa, “Za a gina gidaje na zamani tare da samar musu da asibiti da kayan noma da makarantu. Don haka, ina godiya ga shugaban kasa da mataimakinsa”, inji Gwamna Sani.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya wakilci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya mika sakon jajensu tare da nuna goyon bayansu ga gwamnati da al’ummar Kaduna a wannan lokaci mai cike da damuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
Labarai

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Next Post
Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.