• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan harin bam da aka kai kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya za ta sake gina wa mazauna kauyen gidaje, Makaranta da Asibiti sannan kuma za ta samar musu da kayan Noma.

Shi ma, Gwamna Uba Sani ya baiwa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su tallafi, inda ya ce, gwamnati za ta dauki nauyin kudin duk abinda ake bukata wajen jinya ga wadanda suka jikkata kuma ake duba lafiyarsu a asibitin koyarwa na Barau Dikko da ke jihar Kaduna.

  • Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba
  • A Magance Rashin Aikin Yi A Tsakanin Matasa

Bugu da kari, Gwamnan ya sha alwashin bayar da tallafi na kudi, kula da lafiyar kwakwalwa da kayan masarufi ga marayun da suka rasa masu kula da su a wannan mummunan lamari.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya tarbi wata tawagar jiga-jigan gwamnatin tarayya da suka hada da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, kakakin majalisar wakilai Abbas Tajuddeen, ministan tsaro Mohammed Badaru Abubakar, da shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Gwamna Sani ya kuma mika godiyarsa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta mika ta’aziyyarsa kan ibtila’in inda kuma ya bada umurnin gudanar da bincike cikin gaggawa don gano musabbabin kai harin.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Gwamnan ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, za a bayyanawa Jama’a sakamakon binciken da zarar an kammala, sannan ya jaddada kudirin Shugaba Tinubu na biyan diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da kaddamar da sake gina muhimman ababen more rayuwa a cikin al’ummar Tudun Biri.

Acewarsa, “Za a gina gidaje na zamani tare da samar musu da asibiti da kayan noma da makarantu. Don haka, ina godiya ga shugaban kasa da mataimakinsa”, inji Gwamna Sani.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya wakilci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya mika sakon jajensu tare da nuna goyon bayansu ga gwamnati da al’ummar Kaduna a wannan lokaci mai cike da damuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

Next Post

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

11 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

17 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

18 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

19 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

20 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

21 hours ago
Next Post
Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.