• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin man fetur wajen aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

 

Idris ya bayyana haka ne a Taron Shekara-shekara na Cibiyar Harkokin Jarida ta Duniya (IPI) na 2024 da aka gudanar a Abuja, wanda ke ɗauke da taken “Dimokiraɗiyya, ‘Yancin Kafofin Watsa Labarai, da Muhimmancin Kare Sararin Jama’a na Nijeriya.”

  • Gwamnan Filato Ya Musanta Jita-Jitar Sauya Sheka Zuwa APC
  • Bayan Fara Aikin Matatar Mai Ta Fatakwal, Sai Kuma Me?

A cewar sa, ana amfani da kuɗaɗen tallafin da aka ajiye wajen shirye-shiryen da suka haɗa da bashin ɗalibai, gina ababen more rayuwa, bashi mai rahusa ga jama’a, bunƙasa aikin gona, da kuma shirin jinƙai na musamman.

 

Labarai Masu Nasaba

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Ya ce gwamnatin na mayar da hankali kan cigaban al’umma ta hanyar sauye-sauyen tattalin arziki da zuba jari domin samun cigaba mai ɗorewa ga al’ummar Nijeriya.

 

Ya ce: “Ana karkatar da tiriliyoyin Naira da aka rasa wajen shirye-shiryen tallafi marasa amfani zuwa manyan ajiyoyi, wanda hakan ke bai wa gwamnati damar saka jari a muhimman fannonin tattalin arziki.”

 

Ministan ya bayyana cewa gwamnatin na gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki da suka shafi bunƙasa fannonin tattalin arziki, raya ƙwarewar ɗan’adam, da samar da cigaban tattalin arziki mai inganta kowa.

 

Ya ce babban abu a cikin waɗannan sauye-sauyen shi ne shirin haraji da aka gabatar wanda zai sauƙaƙa biyan haraji tare da rage wa talakawa nauyi.

 

“Ɗaya daga cikin abubuwan da suka ja hankali a wannan gyara shi ne sababbin kariya daga haraji da za su amfani mutane da kamfanoni da dama.”

 

Ya yi nuni da cewa waɗannan sauye-sauyen sun dace da manyan dabarun tattalin arziki, da tabbatar da samun dauwamammen sauyi da samar da Nijeriya mai gasa a duniya.

 

Idris ya kuma yi magana game da mayar da hankali na gwamnatin kan canjin makamashi, yana bayyana shi a matsayin muhimmin ɓangare na shirin cigaban Nijeriya.

 

Ya ce, “Shugaba Tinubu na jagorantar Nijeriya cikin wani sabon mataki na canjin makamashi, inda ya ƙaddamar da shirin shugaban ƙasa na canza ƙasar daga amfani da man fetur zuwa iskar gas ɗin da ake kira Compressed Natural Gas (CNG) a matsayin man motoci da injina.”

 

Wannan sauyi, inji shi, yana rage farashin sufuri zuwa kashi 60, da samar da ayyukan yi, da jawo jari mai yawa.

 

Game da kafofin watsa labarai, Idris ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu tana ba da muhimmanci wajen kare ’yancin kafofin watsa labarai da sararin jama’a.

 

Ya ce: “Tun lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki a watan Mayu 2023, mun sake jaddada aniyar mu ta tabbatarwa da faɗaɗa ‘yancin ‘yan jaridun Nijeriya.”

 

Sai dai, ya ja hankali cewa ’yanci ba shi da amfani idan babu sanin haƙƙi. Ya ce kafofin watsa labarai su kasance masu gudanar da muhawara mai amfani da kuma kula da hukumomi su ɗauki alhakin ayyukan su ba tare da tsananta wa masu ra’ayi mabambanta ba.

 

Idris ya ce: “Kowane ’yanci yana tare da sanin haƙƙi; ’yanci ba shi da ma’ana idan babu iyaka.”

 

Ya kuma bayyana cewa Shugaba Tinubu yana ba da fifiko wajen gyaran tsarin shari’a domin tabbatar da kare haƙƙoƙin ɗan’adam, ciki har da ’yancin faɗar albarkacin baki da haɗin kai.

 

Ya bayyana gyaran a matsayin ginshiƙi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da tabbatar da bin doka a Nijeriya.

 

A ƙarshe, Idris ya ce matakan da gwamnati ke ɗauka suna da matuƙar muhimmanci wajen gina Nijeriya mai arziki, inda ’yancin kafofin watsa labarai da alhakin ‘yan ƙasa ke taka muhimmiyar rawa wajen tsara tafiyar dimokiraɗiyya ta ƙasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Filato Ya Musanta Jita-Jitar Sauya Sheka Zuwa APC

Next Post

Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

Related

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

13 minutes ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

17 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

58 minutes ago
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

1 hour ago
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa
Labarai

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

3 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

6 hours ago
Next Post
Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.