• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin man fetur wajen aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

 

Idris ya bayyana haka ne a Taron Shekara-shekara na Cibiyar Harkokin Jarida ta Duniya (IPI) na 2024 da aka gudanar a Abuja, wanda ke ɗauke da taken “Dimokiraɗiyya, ‘Yancin Kafofin Watsa Labarai, da Muhimmancin Kare Sararin Jama’a na Nijeriya.”

  • Gwamnan Filato Ya Musanta Jita-Jitar Sauya Sheka Zuwa APC
  • Bayan Fara Aikin Matatar Mai Ta Fatakwal, Sai Kuma Me?

A cewar sa, ana amfani da kuɗaɗen tallafin da aka ajiye wajen shirye-shiryen da suka haɗa da bashin ɗalibai, gina ababen more rayuwa, bashi mai rahusa ga jama’a, bunƙasa aikin gona, da kuma shirin jinƙai na musamman.

 

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ya ce gwamnatin na mayar da hankali kan cigaban al’umma ta hanyar sauye-sauyen tattalin arziki da zuba jari domin samun cigaba mai ɗorewa ga al’ummar Nijeriya.

 

Ya ce: “Ana karkatar da tiriliyoyin Naira da aka rasa wajen shirye-shiryen tallafi marasa amfani zuwa manyan ajiyoyi, wanda hakan ke bai wa gwamnati damar saka jari a muhimman fannonin tattalin arziki.”

 

Ministan ya bayyana cewa gwamnatin na gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki da suka shafi bunƙasa fannonin tattalin arziki, raya ƙwarewar ɗan’adam, da samar da cigaban tattalin arziki mai inganta kowa.

 

Ya ce babban abu a cikin waɗannan sauye-sauyen shi ne shirin haraji da aka gabatar wanda zai sauƙaƙa biyan haraji tare da rage wa talakawa nauyi.

 

“Ɗaya daga cikin abubuwan da suka ja hankali a wannan gyara shi ne sababbin kariya daga haraji da za su amfani mutane da kamfanoni da dama.”

 

Ya yi nuni da cewa waɗannan sauye-sauyen sun dace da manyan dabarun tattalin arziki, da tabbatar da samun dauwamammen sauyi da samar da Nijeriya mai gasa a duniya.

 

Idris ya kuma yi magana game da mayar da hankali na gwamnatin kan canjin makamashi, yana bayyana shi a matsayin muhimmin ɓangare na shirin cigaban Nijeriya.

 

Ya ce, “Shugaba Tinubu na jagorantar Nijeriya cikin wani sabon mataki na canjin makamashi, inda ya ƙaddamar da shirin shugaban ƙasa na canza ƙasar daga amfani da man fetur zuwa iskar gas ɗin da ake kira Compressed Natural Gas (CNG) a matsayin man motoci da injina.”

 

Wannan sauyi, inji shi, yana rage farashin sufuri zuwa kashi 60, da samar da ayyukan yi, da jawo jari mai yawa.

 

Game da kafofin watsa labarai, Idris ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu tana ba da muhimmanci wajen kare ’yancin kafofin watsa labarai da sararin jama’a.

 

Ya ce: “Tun lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki a watan Mayu 2023, mun sake jaddada aniyar mu ta tabbatarwa da faɗaɗa ‘yancin ‘yan jaridun Nijeriya.”

 

Sai dai, ya ja hankali cewa ’yanci ba shi da amfani idan babu sanin haƙƙi. Ya ce kafofin watsa labarai su kasance masu gudanar da muhawara mai amfani da kuma kula da hukumomi su ɗauki alhakin ayyukan su ba tare da tsananta wa masu ra’ayi mabambanta ba.

 

Idris ya ce: “Kowane ’yanci yana tare da sanin haƙƙi; ’yanci ba shi da ma’ana idan babu iyaka.”

 

Ya kuma bayyana cewa Shugaba Tinubu yana ba da fifiko wajen gyaran tsarin shari’a domin tabbatar da kare haƙƙoƙin ɗan’adam, ciki har da ’yancin faɗar albarkacin baki da haɗin kai.

 

Ya bayyana gyaran a matsayin ginshiƙi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da tabbatar da bin doka a Nijeriya.

 

A ƙarshe, Idris ya ce matakan da gwamnati ke ɗauka suna da matuƙar muhimmanci wajen gina Nijeriya mai arziki, inda ’yancin kafofin watsa labarai da alhakin ‘yan ƙasa ke taka muhimmiyar rawa wajen tsara tafiyar dimokiraɗiyya ta ƙasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Filato Ya Musanta Jita-Jitar Sauya Sheka Zuwa APC

Next Post

Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

7 minutes ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

49 minutes ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

1 hour ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

5 hours ago
Next Post
Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.