ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Fara Aikin Matatar Mai Ta Fatakwal, Sai Kuma Me?

by Ra'ayinmu
2 years ago
Matatar

Kusan za’ a iya cewa, ‘yan Nijeriya, za su fara samun sauki ganin yadda, matatar man fetur, ta garin Fatawal ta sake farfadowa domin gudanar da aiki.

Hakan ne ya sa dillalan man suka fara yin murna, musamman bayan da kamfanin mai na kasa NNPCL, ya sanar da cewa, an fara yin lodin man daga matatar.

  • Dangote Ya Rage Wa ‘Yan Kasuwa Farashin Man Fetur
  • Matatar Ɗangote Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasar Kamaru

Sai dai, wannan murnar ta dillan man ta sa sun fara yin tunani kan yadda farashin man zai kasance, hakanan su ma ‘yan Nijeriya, ne a cikin irin wannan fargabar ta farashin man.

ADVERTISEMENT

La’akari da yadda gwamnatocin baya suka kasa sake farfado da matatar, amma a yanzu gwamnatin mai ci, ana ganin ta samu nasara kan sake farfado da matatar.

Kazalika ma, me yiyuwa  gwamnatin ta bayar da  umarnin a gyara matatun man  na Warri da kuma Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Bisa martanin da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mayar na dawo da aikin matatar man ta Fatawal, an kuma ruwaito cewa, Tinubu ya umarci NNPCL da ya fara aiki a cikin gaggawa na sake farfado da matatar man ta Fatakwal da kuma sauran matatun biyu.

‘Yan Nijeriya dai, na ci gaba da jira, domin ganin cewar, ko abin da zai auku, zai kasance wani sauki ne, ga matsalar da fannin samar da makamashin kasar ke fuskanta.

Bisa ga dukkan alamu, kafa mamatar mai ta Dangote da kuma farfado da ta Fatakwal, za su share wa ‘yan Nijeriya hawayen, kalubalen da suke fuskanta na karancin samar da man da kuma dakile shigo da man daga ketare.

Shekaru da dama da suka gabata, matatun na Fatakwal, Warri da kuma Kaduna, gwamnatocin baya sun zuba biliyoyin dalali domin sake farfado da su, sai dai, kuma kash! babu wani aikin azo a ganin da aka gudanar.

Bisa wannan ci gaban da aka samu ne, na sake farfado da matatar ta Fatakwal, hakan zai sa a kara samar da man da sauran dangoginsa a Nijeriya, musamman farashinsa.

Sai dai kuma, masu fafutukar a fannin mai da iskar Gas a kasar, da ke son ganin an sake gyaran matatun man kasar, sun kasance suna ja da baya duba, wajen yabawa kan sake farfado da matatar ta Fatakwal.

Sai dai kuma, a ra’ayinsu, idan aka ci gaba da kokarin samar da man a kasar, hakan zai sa a samar da wadatacen sa da kuma sa gasa kan ragin farashin sa.

Amma bisa ra’ayin wannan jaridar, shi ci gaban da aka samu meyiyuwa  ne  daga  karshe, ba zai kai na dogon zango ba, domin fargabar mu ita ce, ‘yan hana ruwa gudu a  fannin, suna iya hanasu yin wani katabus wanda hakan zai dakushe kyakkyawar niyyar da gwamnatin mai ci take da shi, na samar da wadataccen man a kasar

Hakanan ma, wadannan ‘yan hana ruwan gudun na da matukar karfi da dukiyar da za su iya yin amfani da ita domin su hana su yin  abinda ya kamata sanayyarsu, wajen hana abinda ya kamata, na ci gaban da ka samu.

Akasarin ‘yan Nijeriya na sane da cewa, jigajigan ‘yan Nijeriya da ke a fannin man, sun fi mayar da hankali ne ga kasuwar mai ta kasar nan.

A saboda haka, mun sa ido domin mu ga idan har za a iya tuge bututun man Zumar da ke a bakinsu, wanda ya shafe shekaru, yana manne, a bakinsu.

Muna goyon bayan wannan kokarin na sake farfado da matatar ta Fatakwal, matukar dai idan hakan zai samarwa  ‘yan Nijeriya saukin samun man, musamman ma idan an yi la’akari  da matsalar da  cire tallafin mai, ta haifar a kasar.

Sai dai kuma, har yanzu bamu da wani yakinin cewar, sake farfado da matatar man ta Fatakwal, zata samarwa ‘yan Nijeriya wani sauyi.

Amma duk da haka, muna fatan sauyin zai tabbata, musamman  ma yadda a shekarun baya, aka rinka karya lagon fatan ta ‘yan Nijeriya  da kuma barinsu a cikin magagin samun sauki.

Akasarin kayan da ake amfani da su wajen sake farfado da matar man, an sayo su ne, da kudin kasar waje, duk da cewa, mun san irin darajar da kudin kasar ya ke da shi a kasuwar cikin gida da hukuma ta san da ita, da kuma a kasuwar bayan fage.

Bugu da kari, za a dora farashin fanfon man ne, daidai da na farashin danyen mai a kasuwar duniya, wanda daukacin  yin hakan ne, zai kare a kan masu sayen man, saboda kuwa , ba su da wani zabi cewa, illa dole ne, sai su sayi man.

Ko yaya dai abin ya yake,  muna fatar ci  gaban da aka samu zai taimaka wajen inganta samar da mai a wannan kasar tamu.

Babu wani abinda zai karya mana kwarin gwiwa bisa jajicewarmu mu na cewa, farashin man, zai karye warwas, musamman ma saboda da ‘yan Nijeriya su samu saukin sayen man a cikin farashi mai rahusa.

Daga karshe annan jaridar, za ta yi matukar murna ta tabbatar da abinda take da yakini na kara samar da wadataccen man fetur a wannan kasar.

Matatar
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Kwamitin Amintattun PDP Ya Dage Kan Mika Shugabancin Jam’iyyar Ga Sashin Arewa Ta Tsakiya

Kwamitin Amintattun PDP Ya Dage Kan Mika Shugabancin Jam’iyyar Ga Sashin Arewa Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.