• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Ta Fito Da Tsare-tsaren Bunƙasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Ta Fito Da Tsare-tsaren Bunƙasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta fito da wasu tsare-tsare waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar nan tare da samar da aikin yi.

Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Doris Uzoka-Anite, ita ce ta bayyana haka a wurin wani taro na musamman da ‘yan jarida wanda Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, a ƙarƙashin minista Alhaji Mohammed Idris, ta shirya a ranar Juma’a a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Durƙushewar Darajar Naira: Atiku Ya Ba Da Mafita Bayan Ya Caccaki Tinubu
  • Dennis Francis: Bikin Bazara Kyauta Ce Da Kasar Sin Ta Baiwa Duniya

Taron shi ne na biyu a ci gaba da jagorantar ministoci da Idris ke yi domin su riƙa bayyana wa manema labarai irin ci gaban da suka samar a watanni shida da su ka yi, sai kuma bayyana musu irin alƙiblar da ake fuskanta nan gaba.

Tun da farko, Ministan yada labarai, Idris ya buɗe taron da jawabi inda ya ce: “Mun taru a nan domin gina ginshiƙin yarda, amana a tsakaninmu da ‘yan jarida, ta yadda za mu tabbatar cewa, ana sanarwa jama’a abin da muke aiwatarwa.

“Wannan taro ya ba ku damar ku gana kai-tsaye da manyan jami’an gwamnati, ku yi mana tambayoyin da suka cancanta da waɗanda suka shige wa jama’a a duhu.”

Labarai Masu Nasaba

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ministan ya jaddada ƙoƙarin da ma’aikatarsa ke yi wajen yin komai a fili ba tare da ƙumbiya-ƙumbiya ba.

Ya nanata damar samun bayanai da manema labarai ɗin ke da ita, tare da bayyana muhimmiyar rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen isar da saƙonni ga jama’a.

Haka kuma ya ƙara nuna ƙoƙarin tabbatar da yaɗa labarai a kusa da nesa, ta hanyar da aka saba da kuma sabbin hanyoyin na’urorin zamani masu kai saƙonni nesa, nan take.

Yayin da ta ke nata jawabin ga manema labaran, Dakta Doris Uzoka-Anite ta zayyana shirye-shiryen bunƙasa tattalin arzikin da ta bijiro da su, waɗanda ta ce, har samar da ɗimbin ayyukan yi ga ɗimbin ‘yan Nijeriya za su yi.

Ta ce dukkan waɗannan shirye-shirye sun ta’allaƙa ne bisa turbar shikashikai takwas na Shirin Shugaban Ƙasa na Fata Nagari, wanda a Turance ake kira ‘Renewed Hope,’ waɗanda su ka haɗa da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa, samar da ayyukan yi, samar da jari, samar da yanayin gudanar da kasuwanci mai yalwa, rage fatara da talauci.

Ministar ta ce ma’aikatar ta na nan ta na tattauna yadda Nijeriya za ta samu damar cin gajiyar tsarin gudanar da cinikayya a sauƙaƙe tsakanin ƙasashen Afirka, wato AFCFTA.

Ta ce gudanar da wannan kasuwanci kai-tsaye ba tare da tarnaƙi ba zai faɗaɗa kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka, kuma zai ƙara ba da damar shigowar masu zuba jari.

Ta ce a taron baya-bayan nan na 13 na Ministocin Kasuwanci da Cinikayya na AFCFTA, an jaddada matsayin da Nijeriya ke da shi wajen bunƙasar kasuwanci ta hanyar fasahar zamani, sai kuma ƙoƙarin da ƙasar ke yi wajen daƙile haramtaccen ciniki ta hanyar amfani da jiragen ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban tattalin arzikin NijeriyaGyaran masana'antuHaɓaka masana'antu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Bazara Na Shekarar Loong: Alkaluma Sun Bayyana Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin

Next Post

Adadin Sayayya Ta Yanar Gizo Ta Karu Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin

Related

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

39 minutes ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

4 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

5 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

14 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
Next Post
Adadin Sayayya Ta Yanar Gizo Ta Karu Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin

Adadin Sayayya Ta Yanar Gizo Ta Karu Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.