• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gwangwaje Kananan Ma’aikatan Jihar Da Sabbin Gidaje 460

by Hussein Yero
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Gwangwaje Kananan Ma’aikatan Jihar Da Sabbin Gidaje 460
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya mika gidaje dari hudu da sittin (460) ga kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) reshen jihar Zamfara, domin rabawa kananan ma’aikata a jihar.

Gwamna Matawalle ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a wajen bikin na mika rukunin gidajen da ke kan titin Gidan Dawa Daza a Gusau, babban birnin jihar.

  • 2023: Zan Dora Daga Inda Na Tsaya Idan Na Zarce – Matawalle
  • Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

Gwamnan ya bayyana cewa samar da gidajen na daya daga cikin kokarin gwamnatinsa na samar da wurin kwana na dindindin ga ma’aikatan gwamnati a jihar manyan da kananansu”.

“Ya kara da cewa, baya ga samar da gidaje dari hudu da sittin da aka kammala na kananan ma’aikata, za a sake gina wasu gidaje 1000 ga manyan ma’aikatan gwamnati a fadin jihar, inda ya yi nuni da cewa a cikin makon nan ne zai yi bikin kaddamar da harsashin ginin ma’aikatan.

Matwalle ya ce za a gina gidaje dubu daya a Gusau, da nufin magance kalubalen wurin kwana na manyan da kananan ma’aikata a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

“Matawalen ya bayyana matukar damuwarsa kan yadda ma’aikatan gwamnati ke yin ritaya bayan shekaru talatin da biyar suna aiki ba tare da sun mallaki gida ba, wannan ya ce gwamnatinsa za ta magance hakan ta hanyar gina musu gidajan.

A cewar Gwamnan, rukunin farko da na biyu na gidajen da suka kai dari hudu da sittin za a raba su ne ga ma’aikata tare da rage kashi arba’in cikin dari na jimillar kudaden da za a biya cikin shekaru goma.

Gwamna Bello Matawalle ya yi kira ga shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) da su hada kai da ofishin shugaban ma’aikata na jiha da kuma hukumar kula da harkokin kwadago domin tabbatar da adalci wajen rabon gidajen domin amfanar ma’aikatan gwamnati.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, Kwamared Sani Halliru Magajin Rafin Kurya, ya bayyana jin dadinsa ga Gwamnan bisa shirinsa na samar da gidajen kwana ga ma’aikatan da ke aiki.

Kwamared Sani Halliru, a madadin daukacin ma’aikatan jihar ya godewa gwamnan kan yadda ya ceto dubban ma’aikata da iyalansu daga matsalar rashin matsuguni musamman bayan ritayar da suka yi tare da tabbatar wa Gwamna Matawalle goyon bayan ma’aikata da hadin kai domin gwamnatinsa ta samu nasara ga kowa da kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar ‘Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

Next Post

‘Yan Ta’addar Da Suka Yi Garkuwa Da DPO A Jihar Filato Sun Sake Shi

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

11 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

12 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

12 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

13 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

15 hours ago
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yan Ta'addar Da Suka Yi Garkuwa Da DPO A Jihar Filato Sun Sake Shi

LABARAI MASU NASABA

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.