ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Karyata Batun Sace Mutum 500, Ta Jinjina Wa Jami’an Tsaro

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya jinjna wa ƙoƙarin jami’an tsaro na haɗin gwiwa game da sabbin hare-hare da nasarorin da su ke samu a kan ‘yan bindiga a jihar.

A ƙarshen makon da ya gabata, rundunar sojojin ƙasar nan ta aika da wasu ƙarin jami’an ta, a wani yunƙuri na sake fatattakar ayyukan ‘yan bindiga a yankunan da abin ya yi ƙamari a jihar.

  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta Yi Fatali Da Tayin Naira 48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Jihar Legas, Soyannwo Ya Rasu Yana Da Shekara 55

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau yau, ya bayyana dirar mikiyar da sojojin suka yi wa ‘yan bindigar a matsayin mataki na dagula harkokin miyagun ‘yan ta’addan a Zamfara.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta kuma jajanta wa al’ummomin da harin ‘yan bindigar ya shafa a ‘yan kwanakin nan, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar na nan tana ci gaba da baiwa jami’an tsaro cikakken haɗin kai don shawo kan lamarin.

Sanarwar ta ce: “Ayyukan yaƙin da sojoji ke gudanarwa a wuraren da rashin tsaro ya yi ƙamari a Zamfara, abin a yaba ne, musamman bisa la’akari da irin nasarorin da aka samu tun lokacin fara ƙaddamar da munanan hare-hare kan ‘yan ta’addan a ƙarshen makon da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

“Wannan aiki ya samu Gagarumar nasara a yankunan Ƙananan Hukumomin Bungudu, Tsafe, Maru, da Zurmi, wanda ta kai ma hallaka wani ƙasurgumin ɗan ta’adda, Abu Dan Dunkwuifa, wanda ya yi fice wajen addabar wasu ƙauyuka a Bungudu da Maru.

“A ƙauyen Magama Mai Rake ta yankin Dansadau da ke Ƙaramar Hukumar Maru, jami’an tsaron sun samu nasarar hallaka gomomin ‘yan ta’adda.

“Harin da sojoji suka sake kai wa a Nasarawan Burkullu a ƙaramar hukumar Bukkuyum ya yi sanadiyyar ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su a ƙauyukan Kamaru, Tungar Rogo, da Matsare, tare da ƙwato shanu da dama da aka sace.

“Jita-jitar cewa an yi garkuwa da mutane sama da 500 ƙarya ce ta wasu mutane da ba sa son zaman lafiya ya dawo Jihar Zamfara. Mafi akasarin yankunan da ke fama da rashin zaman lafiya a Zamfara na ci gaba da samun taimakon soji, inda ake samun sakamako mai kyau.

Gwamnan ya kuma jajanta wa al’ummar da ’yan bindiga suka kai wa hari a jihar.

“Gwamnatin jihar Zamfara na son nuna alhini ga al’ummomin da ’yan bindiga suka kai wa hari kwanan nan. Mun himmatu sosai wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.

“Gwamnatin mu za ta ci gaba da tallafawa sojojin da ke yaƙi da rashin tsaro tare da bayar da duk wani tallafin gaggawa ga waɗanda rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Sin Ta Amince Da Yankewa Mai Aikata Laifi Mafi Tsanani Hukunci Don Kiyaye Zaman Lafiya Da Tsaro

Sin Ta Amince Da Yankewa Mai Aikata Laifi Mafi Tsanani Hukunci Don Kiyaye Zaman Lafiya Da Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.