• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
Tinubu

Daukacin gwamnatocin kasar nan na kamun kafa wurin Shugaban kasa Bola Tinubu domin ganin ba a aiwatar da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai.

Wasu gwamnoni a lokacin taro da Shugaba Tinubu a fadarsa da ke Abuja, sun kalubalanci bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, inda suka bukaci a magance bashi na biliyoyin dola da ake bin kananan hukumomin kafin fara aiwatar da tsarin.

  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka

Ma’aikatan fadar shugaban kasa sun ce gwamnatocin sun yi amfani da damar cin abinci na bude-baki ga shugaban kasa wajen kamun kafa kuma sake tattaunawa game da bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye, wanda ya samu tsaiko wajen aiwatar da shi.

Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa a lokacin da gwamnatoci suka zo fadar shugaban kasa a ranar Litinin don yi bude-baki, sun nemi ganawar sirri da shugaban kasa, wanda suka yi a ranar Talata da yamma, wanda ya dauki tsawon lokaci tare da shi.

Da yake magana kan batun wanda ya bukaci a sakaye sunansa domin ba a ba shi damar yin magana ba a hukumance, ya ce, “A karshe sun gana da shugaban a ranar Talata don samun mafita. Suna ta yin kokarin yin kamun kafa wurin shugaban kasa na hana kananan hukumomi samun gashin kai.00 / 1:01
“Abin da ke faruwa shi ne batun abubuwa guda biyu. Gwamnatin tarayya tana son a dunga biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa Babban Bankin Nijeriya (CBN), kuma ya kamata dukan kananan hukumomi su bude asusu a CBN.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Amma gwamnoin sun ce a’a. Ba sa son hakan. Sun ce idan kudaden n ya kai ga CBN, ya nuna cewa gwamnatin tarayya ce take kulawa da komi.”

Majiyar ta ce tattaunawar Tinubu da gwamnoni ya bayyana cewa, gwamnonin na bukatar a kai kudaden zuwa bankunan kasuwanci nan take.

“Daya daga cikin gwamnonin ya ce idan har CBN ke kula da asusun, za su bukaci amincewa daga wurin akanta janar na Nijeriya. Wannan yana nufin cewa har yanzu yana karkashin ikon gwamnatin tarayya ne kuma ba su bukatar hakan ya faru. Suna son a kai shi ga banki na kasuwanci. Amma gwamnatin tarayya ta ki amincewa,” in ji majiyar.

Game da sakamakon ganawar, majiyar ta ce, “Sun ce ganawar ta haifar da da mai ido. Amma ban san abin da suka tsaya a kai ba. Suna aiki tare da wasu ma’aikata don su sami hanyar samun fita. Amma abu mafi muhimmanci shi ne, an rike kudaden kananan hukumomi. Ba a biya ba. Saboda wannan dambarwa.”

A tarihi, an dade ana jayayya kan kudaden kananan hukumomi, musamman domin ikon da ke tsakanin jihohi da kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci mai muhimmanci da ya tabbatar da bai wa dukkan kananan hukumomin kasar nan cin gashin kai.

Ya hukuncin ya bayyana cewa dole ne a biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Wannan ya biyo bayan karar da gwamnatin tarayya ta shigar, wadda ta nemi ta daukaka ‘yancin kananan hukumomi kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada.

Kotun kolin ta jaddada cewa ba ya saba wa tsarin kundin mulki gwamnonin jihohi su ci gaba da kula da kudaden kananan hukumomi, inda ta bukaci a dunga tura wa kananan hukumomin kudadensu kai tsayi daga asusun gwamnatin tarayya.

Haka kuma hukuncin ya hada da tsarin samar da shugabannin kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya ne kawai za su iya samun kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

An samar da wannan tsarin ne don magance yadda gwamnonin jihohi suke nada kwamitocin rikon kwarya ko kuma masu kula da ayyukan kananan hukumomi ba tare da yin zabe ba.

A yanzu haka dai, CBN ya bukaci dukkan kananan hukumomi su mika bayanan asusunsu na tsawan shekaru biyu kafin a fara biyansu.

CBN Ya kuma soma bude asusun banki na kananan hukumomi wanda zai dunga tura musu kudadensu kai tsaye.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
nahcon

Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.