ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Daukacin gwamnatocin kasar nan na kamun kafa wurin Shugaban kasa Bola Tinubu domin ganin ba a aiwatar da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai.

Wasu gwamnoni a lokacin taro da Shugaba Tinubu a fadarsa da ke Abuja, sun kalubalanci bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, inda suka bukaci a magance bashi na biliyoyin dola da ake bin kananan hukumomin kafin fara aiwatar da tsarin.

  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka

Ma’aikatan fadar shugaban kasa sun ce gwamnatocin sun yi amfani da damar cin abinci na bude-baki ga shugaban kasa wajen kamun kafa kuma sake tattaunawa game da bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye, wanda ya samu tsaiko wajen aiwatar da shi.

ADVERTISEMENT

Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa a lokacin da gwamnatoci suka zo fadar shugaban kasa a ranar Litinin don yi bude-baki, sun nemi ganawar sirri da shugaban kasa, wanda suka yi a ranar Talata da yamma, wanda ya dauki tsawon lokaci tare da shi.

Da yake magana kan batun wanda ya bukaci a sakaye sunansa domin ba a ba shi damar yin magana ba a hukumance, ya ce, “A karshe sun gana da shugaban a ranar Talata don samun mafita. Suna ta yin kokarin yin kamun kafa wurin shugaban kasa na hana kananan hukumomi samun gashin kai.00 / 1:01
“Abin da ke faruwa shi ne batun abubuwa guda biyu. Gwamnatin tarayya tana son a dunga biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa Babban Bankin Nijeriya (CBN), kuma ya kamata dukan kananan hukumomi su bude asusu a CBN.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“Amma gwamnoin sun ce a’a. Ba sa son hakan. Sun ce idan kudaden n ya kai ga CBN, ya nuna cewa gwamnatin tarayya ce take kulawa da komi.”

Majiyar ta ce tattaunawar Tinubu da gwamnoni ya bayyana cewa, gwamnonin na bukatar a kai kudaden zuwa bankunan kasuwanci nan take.

“Daya daga cikin gwamnonin ya ce idan har CBN ke kula da asusun, za su bukaci amincewa daga wurin akanta janar na Nijeriya. Wannan yana nufin cewa har yanzu yana karkashin ikon gwamnatin tarayya ne kuma ba su bukatar hakan ya faru. Suna son a kai shi ga banki na kasuwanci. Amma gwamnatin tarayya ta ki amincewa,” in ji majiyar.

Game da sakamakon ganawar, majiyar ta ce, “Sun ce ganawar ta haifar da da mai ido. Amma ban san abin da suka tsaya a kai ba. Suna aiki tare da wasu ma’aikata don su sami hanyar samun fita. Amma abu mafi muhimmanci shi ne, an rike kudaden kananan hukumomi. Ba a biya ba. Saboda wannan dambarwa.”

A tarihi, an dade ana jayayya kan kudaden kananan hukumomi, musamman domin ikon da ke tsakanin jihohi da kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci mai muhimmanci da ya tabbatar da bai wa dukkan kananan hukumomin kasar nan cin gashin kai.

Ya hukuncin ya bayyana cewa dole ne a biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Wannan ya biyo bayan karar da gwamnatin tarayya ta shigar, wadda ta nemi ta daukaka ‘yancin kananan hukumomi kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada.

Kotun kolin ta jaddada cewa ba ya saba wa tsarin kundin mulki gwamnonin jihohi su ci gaba da kula da kudaden kananan hukumomi, inda ta bukaci a dunga tura wa kananan hukumomin kudadensu kai tsayi daga asusun gwamnatin tarayya.

Haka kuma hukuncin ya hada da tsarin samar da shugabannin kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya ne kawai za su iya samun kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

An samar da wannan tsarin ne don magance yadda gwamnonin jihohi suke nada kwamitocin rikon kwarya ko kuma masu kula da ayyukan kananan hukumomi ba tare da yin zabe ba.

A yanzu haka dai, CBN ya bukaci dukkan kananan hukumomi su mika bayanan asusunsu na tsawan shekaru biyu kafin a fara biyansu.

CBN Ya kuma soma bude asusun banki na kananan hukumomi wanda zai dunga tura musu kudadensu kai tsaye.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
nahcon

Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.