ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Daukacin gwamnatocin kasar nan na kamun kafa wurin Shugaban kasa Bola Tinubu domin ganin ba a aiwatar da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai.

Wasu gwamnoni a lokacin taro da Shugaba Tinubu a fadarsa da ke Abuja, sun kalubalanci bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, inda suka bukaci a magance bashi na biliyoyin dola da ake bin kananan hukumomin kafin fara aiwatar da tsarin.

  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka

Ma’aikatan fadar shugaban kasa sun ce gwamnatocin sun yi amfani da damar cin abinci na bude-baki ga shugaban kasa wajen kamun kafa kuma sake tattaunawa game da bai wa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye, wanda ya samu tsaiko wajen aiwatar da shi.

ADVERTISEMENT

Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa a lokacin da gwamnatoci suka zo fadar shugaban kasa a ranar Litinin don yi bude-baki, sun nemi ganawar sirri da shugaban kasa, wanda suka yi a ranar Talata da yamma, wanda ya dauki tsawon lokaci tare da shi.

Da yake magana kan batun wanda ya bukaci a sakaye sunansa domin ba a ba shi damar yin magana ba a hukumance, ya ce, “A karshe sun gana da shugaban a ranar Talata don samun mafita. Suna ta yin kokarin yin kamun kafa wurin shugaban kasa na hana kananan hukumomi samun gashin kai.00 / 1:01
“Abin da ke faruwa shi ne batun abubuwa guda biyu. Gwamnatin tarayya tana son a dunga biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa Babban Bankin Nijeriya (CBN), kuma ya kamata dukan kananan hukumomi su bude asusu a CBN.

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

“Amma gwamnoin sun ce a’a. Ba sa son hakan. Sun ce idan kudaden n ya kai ga CBN, ya nuna cewa gwamnatin tarayya ce take kulawa da komi.”

Majiyar ta ce tattaunawar Tinubu da gwamnoni ya bayyana cewa, gwamnonin na bukatar a kai kudaden zuwa bankunan kasuwanci nan take.

“Daya daga cikin gwamnonin ya ce idan har CBN ke kula da asusun, za su bukaci amincewa daga wurin akanta janar na Nijeriya. Wannan yana nufin cewa har yanzu yana karkashin ikon gwamnatin tarayya ne kuma ba su bukatar hakan ya faru. Suna son a kai shi ga banki na kasuwanci. Amma gwamnatin tarayya ta ki amincewa,” in ji majiyar.

Game da sakamakon ganawar, majiyar ta ce, “Sun ce ganawar ta haifar da da mai ido. Amma ban san abin da suka tsaya a kai ba. Suna aiki tare da wasu ma’aikata don su sami hanyar samun fita. Amma abu mafi muhimmanci shi ne, an rike kudaden kananan hukumomi. Ba a biya ba. Saboda wannan dambarwa.”

A tarihi, an dade ana jayayya kan kudaden kananan hukumomi, musamman domin ikon da ke tsakanin jihohi da kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci mai muhimmanci da ya tabbatar da bai wa dukkan kananan hukumomin kasar nan cin gashin kai.

Ya hukuncin ya bayyana cewa dole ne a biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Wannan ya biyo bayan karar da gwamnatin tarayya ta shigar, wadda ta nemi ta daukaka ‘yancin kananan hukumomi kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada.

Kotun kolin ta jaddada cewa ba ya saba wa tsarin kundin mulki gwamnonin jihohi su ci gaba da kula da kudaden kananan hukumomi, inda ta bukaci a dunga tura wa kananan hukumomin kudadensu kai tsayi daga asusun gwamnatin tarayya.

Haka kuma hukuncin ya hada da tsarin samar da shugabannin kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya ne kawai za su iya samun kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

An samar da wannan tsarin ne don magance yadda gwamnonin jihohi suke nada kwamitocin rikon kwarya ko kuma masu kula da ayyukan kananan hukumomi ba tare da yin zabe ba.

A yanzu haka dai, CBN ya bukaci dukkan kananan hukumomi su mika bayanan asusunsu na tsawan shekaru biyu kafin a fara biyansu.

CBN Ya kuma soma bude asusun banki na kananan hukumomi wanda zai dunga tura musu kudadensu kai tsaye.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna
  • Sulaiman
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
  • Sulaiman
    Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

MASU ALAKA

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Next Post
nahcon

Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.