• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sun caccaki gwamnatin tarayya kan matsin rayuwa tare da yin kira ta kawo matakan gaggawa da za su kawar da matsalar tattalin arziki da kalubalan tsaro da ke addabar kasar nan.

Shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed shi ya yi wannan kira lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ganawar gwamnonin jam’iyyar adawa da ya gudana a gidan gwamnatin Jihar Oyo da ke Abuja.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Da yake amsa tambayoyi kan tsadar rayuwa da ake ciki, gwamnan ya bayyana cewa sun goyi bayan cire tallafin man fetur da wannan gwamnati ta yi ne bisa fatan za a samu saukin rayuwa, amma lamarin ba haka yake ba.

Ya bayyana damuwarsa kan yadda darajar naira ke kara zubewa kasa warwar, yayin da ake ci gaba da samun tsadar rayuwa.

A cewarsa, “Lallai muna caccakan munanan manufofin gwamnatin tarayya. Amma a bangare daya kuma, mun goyi bayan wannan gwamnati na cire tallafin mai, saboda muna da tabbacin cewa hakan shi ne manufa, idan har muka hada kai, to za a samu mafita kan wannan lamari.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Amma muna ganin shi ne ya kawo faduwar daragar naira wanda ya haddasa tsadar rayuwa, inda a yanzu muke kafada da kafada da kasar Benezuela.

Saboda haka, muna hamayya da munanan manufofin gwamnatin tarayya ba tare da mun zagi kowa ba.

“Mun dauki wannan mataki ne domin ceto ‘yan Nijeriya da kuma kasar nan ta yadda za mu yi wasu abubuwa domin taimaka wa kawunanmu.”

Tun da farko, kungiyar ta jaddata manufarta na kirkiran ‘yansandar jihohi a matsayin wani taki da zai kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya.

“Wannan tattaunawar ta shafi sake duba yadda kasa ke ciki da kuma matsin rayuwa da ‘yan Nijeriya suka tsinci kansu a ciki sakamakon matsin tattalin arziki da kalubalan tsaro da kasar ke fuskanta. Wannan kungiyarmu tana kira ga gwamnatin tarayya ta bullo da wasu shirye-shirye da zai kunshi dukkanin gwamnatocin kasar nan domin kawo karshen lamarin.

“Gwamnonin PDP za su ci gaba da yin iya bakin kokarinsu wajen kawo karshen matsalar tsaro domin bayar da kariya ga al’ummar kasar nan. Muna jaddada aniyarmu na yin kira da a kirkiro ‘yansandar jihohi domin kaucewa duk wata hanya ta yin amfani da ofishi ba bisa ka’ida ba ga bangarorin gwamnati.

“Lallain kungiyarmu ta koka kan yadda darajar naira ya karye tare da yinkira ga hukumomin kula da kudade da su ballo da mafita,” in ji kungiyar gwamnonin PDP.

Gwamnonin PDP sun amince da kwamitin gudanarwar jam’iyyar na kasakarkashin jagorancin mukaddasin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum. Haka kuma sun bukaci kwamitin ya kira taron gaggawa na k asa ba da jimawa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland

Next Post

Wike Zai Sake Kwace Filaye Da Dama A Abuja

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 week ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

Wike Zai Sake Kwace Filaye Da Dama A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.