• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

byYusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sun caccaki gwamnatin tarayya kan matsin rayuwa tare da yin kira ta kawo matakan gaggawa da za su kawar da matsalar tattalin arziki da kalubalan tsaro da ke addabar kasar nan.

Shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed shi ya yi wannan kira lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ganawar gwamnonin jam’iyyar adawa da ya gudana a gidan gwamnatin Jihar Oyo da ke Abuja.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Da yake amsa tambayoyi kan tsadar rayuwa da ake ciki, gwamnan ya bayyana cewa sun goyi bayan cire tallafin man fetur da wannan gwamnati ta yi ne bisa fatan za a samu saukin rayuwa, amma lamarin ba haka yake ba.

Ya bayyana damuwarsa kan yadda darajar naira ke kara zubewa kasa warwar, yayin da ake ci gaba da samun tsadar rayuwa.

A cewarsa, “Lallai muna caccakan munanan manufofin gwamnatin tarayya. Amma a bangare daya kuma, mun goyi bayan wannan gwamnati na cire tallafin mai, saboda muna da tabbacin cewa hakan shi ne manufa, idan har muka hada kai, to za a samu mafita kan wannan lamari.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Amma muna ganin shi ne ya kawo faduwar daragar naira wanda ya haddasa tsadar rayuwa, inda a yanzu muke kafada da kafada da kasar Benezuela.

Saboda haka, muna hamayya da munanan manufofin gwamnatin tarayya ba tare da mun zagi kowa ba.

“Mun dauki wannan mataki ne domin ceto ‘yan Nijeriya da kuma kasar nan ta yadda za mu yi wasu abubuwa domin taimaka wa kawunanmu.”

Tun da farko, kungiyar ta jaddata manufarta na kirkiran ‘yansandar jihohi a matsayin wani taki da zai kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya.

“Wannan tattaunawar ta shafi sake duba yadda kasa ke ciki da kuma matsin rayuwa da ‘yan Nijeriya suka tsinci kansu a ciki sakamakon matsin tattalin arziki da kalubalan tsaro da kasar ke fuskanta. Wannan kungiyarmu tana kira ga gwamnatin tarayya ta bullo da wasu shirye-shirye da zai kunshi dukkanin gwamnatocin kasar nan domin kawo karshen lamarin.

“Gwamnonin PDP za su ci gaba da yin iya bakin kokarinsu wajen kawo karshen matsalar tsaro domin bayar da kariya ga al’ummar kasar nan. Muna jaddada aniyarmu na yin kira da a kirkiro ‘yansandar jihohi domin kaucewa duk wata hanya ta yin amfani da ofishi ba bisa ka’ida ba ga bangarorin gwamnati.

“Lallain kungiyarmu ta koka kan yadda darajar naira ya karye tare da yinkira ga hukumomin kula da kudade da su ballo da mafita,” in ji kungiyar gwamnonin PDP.

Gwamnonin PDP sun amince da kwamitin gudanarwar jam’iyyar na kasakarkashin jagorancin mukaddasin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum. Haka kuma sun bukaci kwamitin ya kira taron gaggawa na k asa ba da jimawa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

Wike Zai Sake Kwace Filaye Da Dama A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version