• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Da Ya Kawo Sauyin Kula Da Muhalli A Nijeriya 2024: Balarabe Abbas Lawal

byLeadership Hausa
10 months ago
Gwarzo

Ministan Muhalli a Nijeriya, Alhaji Balarabe Abbas Lawal ne ya yi nasarar zama gwarzon shekara ta 2024 na Jaridar Leadership, saboda hangen nesansa da kyawawan manufofinsa da ya aiwatar a ma’aikatarsa ta muhalli, wanda ya yi tasiri da kawo sauyi a ɓangaren kula da muhalli a Nijeriya a ƙarƙashin gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Samar da Kyakkyawan tsari da zuwa da sababbin sauye-sauye waje kula da muhalli, ya bayar da gudummawa sosai kan tsaron kasa da samar da bunƙasar tattalin arziƙin ƙasa, ya sa Balarabe Lawal ya zama fitila a tsakanin takwarorinsa ministoci.

  • Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526
  • Gwamna Radda Ya Kaddamar Da Shirin Ci Gaban Al’umma

Manyan nasarorin da Lawal ya samu sun biyo bayan sabon tsarinsa na yaki da sauyin yanayi da farfaɗo da muhalli a Nijeriya. A Jagorancinsa ya ƙaddamar da wasu tsare-tsare da za su magance matsalolin da suka daɗe ana fama da su a Nijeriya, tare da aiwatar da sababbi da ya da za su magance barazana ga muhalli.

Nasarar da aka samu ta tsaftace Ogoni, lamarin da ya ƙi ci- ya ƙi cinyewa, amma a ƙarƙashin jagorancin Lawal an ga ƙarshensa, ya samu yabo iri-iri daga al’umma daban-daban a ciki da wajen ƙasa kan wannan gagarumin aiki.

Lawal ya samu yabo da goyon bayan al’umma, ta hanyar samun hadin kan masu ruwa da tsaki daga cikin shugabannin yayin kaddamar da ayyukan ma’aikatarsa, kamar tsarin samar da tsaftataccen ruwa a ƙarƙashin Cibiyar Inganta Muhalli a Wiiyakara. Wannan shaida ce ga sadaukarwarsa don farfaɗo da cibiyoyin inganta muhalli da jin daɗin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Saurin fahimtar matsalar sare Bishiyoyi, Lawal ya jagoranci rarraba irin Bishiyoyi miliyan 45 a faɗin ƙasa baki ɗaya. Wannan gagarumin ƙoƙarin yaƙi da sare Bishiyoyi, da kuma sake shuka wasu a gandun daji ya taimaka wajen yaƙi da kwararowar hamada da inganta yanayin muhalli.

Shirin ‘Agro-Climatic Resilience in SemiArid Landscapes (ACReSAL),’ shirin ya dawo da darajar kadada 350,000 da ta gurbace. Wannan yunƙurin na nuna kishin al’umma da ƙasa da ake fama da kwararowar hamada da sauyin yanayi.

Fahimtar muhimmancin tattalin arzikin Nijeriya a tafkin Chadi, Lawal ya jagoranci yunkurin ƙasa da ƙasa na dawo da darajar yanayin tafkin. Haɗin guiwa tare da abokan hulɗa na duniya daga EU da UAE da Kanada, ya samar da nasarori masu muhimmanci da suka haɗa da dabarar datsewa da sauyawa ruwa hanya, da kuma samar masa da yanayin kula mai dorewa. Lallai wannan shugaba yana da zimma da ruhin aiki da kuma kishin ganin ingantaccen yanayi mai dorewa a Nijeriya.

Saboda sadaukarwarsa da kula da muhalli, ya tabbatarwa duniya cewa jagoranci nagari zai haifar da sakamako na ban mamaki. Don kishin ƙasa da jagoranci nagari wajen gina ƙasa da ci gabanta mai dorewa, Balarabe Abbas Lawal shi ya lashe kyautar LEADERSHIP na Gwarzon Jagoran Kula da Muhalli na Shekarar 2024.

Lawal ya sanya Nijeriya a babban matsayi mai daraja a ƙasashen duniya kan shirin kula da yanayi da muhalli a ƙawancen duniya (COP28).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Oluwatobi Ajayi

Gwarzon Shugaban Kamfanoni Masu Zaman Kansu Na 2024: Oluwatobi Ajayi

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version