• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

by Sadiq
3 years ago
Tambuwal

Mataimakiya ta musamman ga Gwamna Aminu Waziri Tambuwal kan harkokin Ilimin mata, Hajiya Aishat Maina ta rasu.

Ta rasu ne bayan halartar taron gangamin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP da ya gudana a Jihar Sakkwato a ranar Talata.

  • Sin Na Tsayawa Tsayin Daka Kan Yaki Da Ta’addanci
  • Da Dumi-Dumi: Mahara Sun Kashe DPO Da Wasu A Benue

Leadership Hausa ta gano cewa, ta shiga cikin turmutsitsin da ya afku a kofar fitta daga filin taron.

“Wani direban babur ne ya fado daga kan babur dinsa a hanyar fita dava filin wanda hakan ya haifar da mumunan turmutsutsu, inda mutane suka fado kan juna. Tana daya daga cikin wadanda abin ya shafa,” cewar wata majiya.

Da yake tabbatar da hakan, shugaban kungiyar masu ba da shawara na musamman, Ibrahim Magaji Gusau, ya ce an ceto marigayiyar, inda aka garzaya da ita Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato domin yi mata magani.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

“Abun takaici ta mutu ‘yan mintuna kadan bayan kai ta asibiti,” in ji shi Magaji, wanda ya bayyana ta a matsayin mai kwazo da hazaka.

“Ko a lokacin taron, muna tare, ba tare da sanin cewa hakan zai zama taronmu na karshe ba,” in ji shi, ya yi mata addu’ar Allah ya gafarta mata kurakuranta, ya kuma sanya ta a Jannatul Firdaus.

Marigayiyar dai tsohuwar shugabar kungiyar ‘yan jarida ce ta kasa (NAWOJ) a Jihar Sakkwato.

Ta kuma kasance tsohuwar mai bai wa Gwamna Aminu Tambuwal shawara kan sabbin kafafen yada labarai kafin a dauke ta zuwa Hukumar Ilimi ta Mata.

Tsohon Shugaban Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) a Jihar Sakkwato, Isa Abubakar Shuni, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar ‘yar jaridar ba zato ba tsammani, inda ya bayyana cewa ta ba da gudunmawa sosai ga harkar aikin jarida a jihar.

Ta rasu ta bar ‘ya’ya uku da kuma iyayenta tsofaffi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya – Atiku 

Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya - Atiku 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.