• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON

by Abubakar Abba
3 years ago
Hajjin 2023

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), ta ce kowane maniyyaci da zai je aikin Hajjin 2003, zai biya Naira miliyan 2.89.

Shugaban hukumar na kasa, Zikrullah Hassan ne, ya sanar da hakan a yau Juma’a, inda ya danganta hakan da hauhawar farashin kaya a Nijeriya da kuma Saudiyya.

  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade
  • Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Hassan, ya ce an tsara farashin bisa kashi takwas, inda jihohin Borno da Yobe, ke da karancin farashi sai kuma jihohin Legas da Ogun na su farashin ya fi yawa, wanda ya kai Naira miliyan 2.99.

Rahotannin sun bayyana cewa, karin kudin hajjin ya kai sama da Naira 300,000, inda aka kwatanta da kudin da alhasai suka biya a 2022.

Ya kara da cewa, farashin aikin hajjin, tsadarsa kashi takwas ne, inda maniyyacin da ya fito daga Maiduguri da wanda ya fito daga Yola, kowanensu zai biya Naira miliyan 2.89 sauran wadanda suka fito daga jihohin Arewa kuwa, kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.919.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

A cewarsa, kudancin kasar kuwa, na da farashin kashi shida, inda Jihar Edo da sauran jihohin da ke a Kudu maso Kudu da kuma a Kudu maso Gabas kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.9, inda kuma wadanda suka fito daga jihohin Ekiti da Ondo, kowane zai biya Naira miliyan 2.88.

Kazalika, ya ce kowane maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Osun, zai biya Naira miliyan 2.99, inda maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Kuros Ribas zai biya Naira miliyan 2.943, haka kowane maniyyacin daya da ya fito daga jihar Legas, Ogun da Oyo, zai biya Naira miliyan 2.99.

Ya ce an samu bambamcin farashin ne domin jihohin da ke Arewa sun fi makwabtaka da Saudiyya fiye da sauran jihohin da ke a kudancin kasar nan, inda kuma masaukan maniyyatan da kowace jiha za ta kama ke nuna abin da ya kamata maniyyaci zai biya.

Bugu da kari, kamfanonin jiragen saman da aka sahale wa su yi jigilar maniyyatan zuwa kasar mai tsarki su ne; Air Peace, Azman Air, Fly Nas, Aero Contractors da kuma Max Air, inda Arik Air da kuma Value jet.

Shugaban, ya ce za rufe rumbun adana bayanan hukumar ga wadanda suka yi zabi su shiga shirin zuwa kasar mai tsarki ta hanyar zuba kudin adashin gata a ranar 21 ga watan Afirilu, 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
Manyan Labarai

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Next Post
Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.