ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON

by Abubakar Abba
3 years ago
Hajjin 2023

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), ta ce kowane maniyyaci da zai je aikin Hajjin 2003, zai biya Naira miliyan 2.89.

Shugaban hukumar na kasa, Zikrullah Hassan ne, ya sanar da hakan a yau Juma’a, inda ya danganta hakan da hauhawar farashin kaya a Nijeriya da kuma Saudiyya.

  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade
  • Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Hassan, ya ce an tsara farashin bisa kashi takwas, inda jihohin Borno da Yobe, ke da karancin farashi sai kuma jihohin Legas da Ogun na su farashin ya fi yawa, wanda ya kai Naira miliyan 2.99.

ADVERTISEMENT

Rahotannin sun bayyana cewa, karin kudin hajjin ya kai sama da Naira 300,000, inda aka kwatanta da kudin da alhasai suka biya a 2022.

Ya kara da cewa, farashin aikin hajjin, tsadarsa kashi takwas ne, inda maniyyacin da ya fito daga Maiduguri da wanda ya fito daga Yola, kowanensu zai biya Naira miliyan 2.89 sauran wadanda suka fito daga jihohin Arewa kuwa, kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.919.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

A cewarsa, kudancin kasar kuwa, na da farashin kashi shida, inda Jihar Edo da sauran jihohin da ke a Kudu maso Kudu da kuma a Kudu maso Gabas kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.9, inda kuma wadanda suka fito daga jihohin Ekiti da Ondo, kowane zai biya Naira miliyan 2.88.

Kazalika, ya ce kowane maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Osun, zai biya Naira miliyan 2.99, inda maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Kuros Ribas zai biya Naira miliyan 2.943, haka kowane maniyyacin daya da ya fito daga jihar Legas, Ogun da Oyo, zai biya Naira miliyan 2.99.

Ya ce an samu bambamcin farashin ne domin jihohin da ke Arewa sun fi makwabtaka da Saudiyya fiye da sauran jihohin da ke a kudancin kasar nan, inda kuma masaukan maniyyatan da kowace jiha za ta kama ke nuna abin da ya kamata maniyyaci zai biya.

Bugu da kari, kamfanonin jiragen saman da aka sahale wa su yi jigilar maniyyatan zuwa kasar mai tsarki su ne; Air Peace, Azman Air, Fly Nas, Aero Contractors da kuma Max Air, inda Arik Air da kuma Value jet.

Shugaban, ya ce za rufe rumbun adana bayanan hukumar ga wadanda suka yi zabi su shiga shirin zuwa kasar mai tsarki ta hanyar zuba kudin adashin gata a ranar 21 ga watan Afirilu, 2023.

Hajjin 2023
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.