ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON

by Abubakar Abba
3 years ago
Hajjin 2023

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), ta ce kowane maniyyaci da zai je aikin Hajjin 2003, zai biya Naira miliyan 2.89.

Shugaban hukumar na kasa, Zikrullah Hassan ne, ya sanar da hakan a yau Juma’a, inda ya danganta hakan da hauhawar farashin kaya a Nijeriya da kuma Saudiyya.

  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade
  • Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Hassan, ya ce an tsara farashin bisa kashi takwas, inda jihohin Borno da Yobe, ke da karancin farashi sai kuma jihohin Legas da Ogun na su farashin ya fi yawa, wanda ya kai Naira miliyan 2.99.

ADVERTISEMENT

Rahotannin sun bayyana cewa, karin kudin hajjin ya kai sama da Naira 300,000, inda aka kwatanta da kudin da alhasai suka biya a 2022.

Ya kara da cewa, farashin aikin hajjin, tsadarsa kashi takwas ne, inda maniyyacin da ya fito daga Maiduguri da wanda ya fito daga Yola, kowanensu zai biya Naira miliyan 2.89 sauran wadanda suka fito daga jihohin Arewa kuwa, kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.919.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

A cewarsa, kudancin kasar kuwa, na da farashin kashi shida, inda Jihar Edo da sauran jihohin da ke a Kudu maso Kudu da kuma a Kudu maso Gabas kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.9, inda kuma wadanda suka fito daga jihohin Ekiti da Ondo, kowane zai biya Naira miliyan 2.88.

Kazalika, ya ce kowane maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Osun, zai biya Naira miliyan 2.99, inda maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Kuros Ribas zai biya Naira miliyan 2.943, haka kowane maniyyacin daya da ya fito daga jihar Legas, Ogun da Oyo, zai biya Naira miliyan 2.99.

Ya ce an samu bambamcin farashin ne domin jihohin da ke Arewa sun fi makwabtaka da Saudiyya fiye da sauran jihohin da ke a kudancin kasar nan, inda kuma masaukan maniyyatan da kowace jiha za ta kama ke nuna abin da ya kamata maniyyaci zai biya.

Bugu da kari, kamfanonin jiragen saman da aka sahale wa su yi jigilar maniyyatan zuwa kasar mai tsarki su ne; Air Peace, Azman Air, Fly Nas, Aero Contractors da kuma Max Air, inda Arik Air da kuma Value jet.

Shugaban, ya ce za rufe rumbun adana bayanan hukumar ga wadanda suka yi zabi su shiga shirin zuwa kasar mai tsarki ta hanyar zuba kudin adashin gata a ranar 21 ga watan Afirilu, 2023.

Hajjin 2023
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.