ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Buhari

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Kwankwaso ya zargi Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gaza gudanar da sahihin zabe a 2023.

Ya ce shugaban kasar bai yi abin da ya dace ba don ganin an gudanar da sahihin zabe.
Ya kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin magudin zabe a wasu jihohi, musamman zaben shugaban kasa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Kasa, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Kwankwaso ya yi zargin cewa sakamakon zaben da aka kammala ba zabin ‘yan Nijeriya ba ne.

ADVERTISEMENT

Da yake magana a taron farko bayan zaben 2023 na majalisar zartaswar jam’iyyar NNPP ta kasa, tsohon ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Kano har sau biyu ya koka da yadda ‘yan Nijeriya ba su sami damar cin moriyar canji mai kyau da suke nema ba.

Ya kuma bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun gaji da jam’iyya mai mulki, domin ya ci gaba da cewa APC ta koma sayen kuri’u da kudaden gida da na waje, da kuma yin amfani da ‘yan daba wajen murkushe ‘yancin zabe.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sanata Kwankwaso ya yi kira na musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ya zarga da shigo da ‘yan daba daga jihohi da kasashe makwabta, kamar yadda ya kuma yi nuni cewa akwai sa hannun wasu jami’an tsaro a tashe-tashen hankula da suka shafi zabe.

A yayin da yake zargin ‘yan siyasa da cewa da gangan suke talauta ‘yan Nijeriya domin su sayi kuri’a a lokacin zabe, ya yi gargadin a guji cin nasara ko ta halin kaka, domin ya koka da yadda rashin adalci ke haifar da ‘yan fashi, Boko Haram, da sauran rikice-rikicen da suka addabi kasar nan.

Jagoran NNPP na kasa ya yi nadamar cewa akwai abubuwa da yawa da ke damun dimokuradiyyar Nijeriya. Inda ya ce mutane kalilan ne ke amfana da tsarin.

Yayin da yake gargadin cewa, “Nijeriya tamu ce kuma babu wanda ya isa ya kore mu a ciki “, jagoran ya bayyana fatansa cewa bangaren shari’a ya kasance wuri mafi kyau a gare mu duka.”

Ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar NNPP da su yi amfani da damar da aka ba su kafin zaben 2027, su zage-dantse wajen gudanar da ayyukan da suka dace a mazabarsu.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi kira ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta inganta harkokinta wajen gudanar da zabuka a nan gaba, inda ya koka da yadda ba a buga tambarin jam’iyyar a kan takardun zabe ba, don haka ya sa jam’iyyarsa ta rasa kuri’an magoya bayanta a wasu wurare.

Ya bayyana cewa hatta wasu masu sa ido na kasa da kasa sun kasa tantance tambarin jam’iyyar NNPP da ke cikin takardun zabe.

Don haka, ya yaba wa jam’iyyar bisa nasarorin da suka samu, inda ya bayyana cewa mutane da dama ne ke neman shiga kafin zaben 2027.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

'Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.