ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Buhari

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Kwankwaso ya zargi Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gaza gudanar da sahihin zabe a 2023.

Ya ce shugaban kasar bai yi abin da ya dace ba don ganin an gudanar da sahihin zabe.
Ya kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin magudin zabe a wasu jihohi, musamman zaben shugaban kasa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Kasa, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Kwankwaso ya yi zargin cewa sakamakon zaben da aka kammala ba zabin ‘yan Nijeriya ba ne.

ADVERTISEMENT

Da yake magana a taron farko bayan zaben 2023 na majalisar zartaswar jam’iyyar NNPP ta kasa, tsohon ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Kano har sau biyu ya koka da yadda ‘yan Nijeriya ba su sami damar cin moriyar canji mai kyau da suke nema ba.

Ya kuma bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun gaji da jam’iyya mai mulki, domin ya ci gaba da cewa APC ta koma sayen kuri’u da kudaden gida da na waje, da kuma yin amfani da ‘yan daba wajen murkushe ‘yancin zabe.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sanata Kwankwaso ya yi kira na musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ya zarga da shigo da ‘yan daba daga jihohi da kasashe makwabta, kamar yadda ya kuma yi nuni cewa akwai sa hannun wasu jami’an tsaro a tashe-tashen hankula da suka shafi zabe.

A yayin da yake zargin ‘yan siyasa da cewa da gangan suke talauta ‘yan Nijeriya domin su sayi kuri’a a lokacin zabe, ya yi gargadin a guji cin nasara ko ta halin kaka, domin ya koka da yadda rashin adalci ke haifar da ‘yan fashi, Boko Haram, da sauran rikice-rikicen da suka addabi kasar nan.

Jagoran NNPP na kasa ya yi nadamar cewa akwai abubuwa da yawa da ke damun dimokuradiyyar Nijeriya. Inda ya ce mutane kalilan ne ke amfana da tsarin.

Yayin da yake gargadin cewa, “Nijeriya tamu ce kuma babu wanda ya isa ya kore mu a ciki “, jagoran ya bayyana fatansa cewa bangaren shari’a ya kasance wuri mafi kyau a gare mu duka.”

Ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar NNPP da su yi amfani da damar da aka ba su kafin zaben 2027, su zage-dantse wajen gudanar da ayyukan da suka dace a mazabarsu.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi kira ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta inganta harkokinta wajen gudanar da zabuka a nan gaba, inda ya koka da yadda ba a buga tambarin jam’iyyar a kan takardun zabe ba, don haka ya sa jam’iyyarsa ta rasa kuri’an magoya bayanta a wasu wurare.

Ya bayyana cewa hatta wasu masu sa ido na kasa da kasa sun kasa tantance tambarin jam’iyyar NNPP da ke cikin takardun zabe.

Don haka, ya yaba wa jam’iyyar bisa nasarorin da suka samu, inda ya bayyana cewa mutane da dama ne ke neman shiga kafin zaben 2027.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

'Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.