Wani mahajjaci daga Jihar Kano mai suna Shu’aibu Jibrin ya rasu a birnin Makka da ke ƙasar Saudiyya, kwana ɗaya kafin a fara gudanar da ibadar Hajji ta shekarar 2025.
Mai magana da yawun Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, Malam Suleiman Dederi, ne ya tabbatar da rasuwar Jibrin, inda ya ce marigayin ya rasu a ranar Talata bayan wata gajeriyar rashin lafiya.
- Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
- Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Ɗaya daga cikin ‘yan uwansa, Sama’uddin Aliyu Kadawa, wanda shi ma na cikin mahajjatan, ya shaida wa manema labarai a Makka cewa marigayin yana cikin ƙoshin lafiya kafin tafiyarsu daga gida.
“Bayan ya fara jin jiki, an kai shi Asibitin Sarki Abdulazeez inda ya kwana biyu kafin a sallame shi saboda ya samu lafiya.
“Amma daga baya sai yanayinsa ya ƙara taɓarɓarewa, aka sake garzayawa da shi asibiti. Duk da ƙoƙarin likitocin Nijeriya da na asibitin Saudiyya, ya rasu da misalin ƙarfe 2:50 na dare,” in ji shi.
Aliyu, ya bayyana cewa Jibrin manomi ne daga ƙauyen Gargai da ke ƙaramar hukumar Bebeji a Kano.
Ya kuma ce yana fama da cutar gyambon ciki da hawan jini.
Likitoci sun bayyana cewa rasuwarsa ta faru ne sakamakon bugun zuciya da gazawar zuciya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp