• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Ake Ciki Bayan Wata Hudu Da Juyin Mulkin Nijar

•Murnar Wasu Ta Koma Ciki – Yusuf Buzu

by Bello Hamza
2 years ago
Nijar

A ranar 26 ga watan Yulin shekara ta 2023, sojoji daga masu gadin fadar shugaban kasar, Nijar suka tsare shugaba Mohamed Bazoum, yayin da wasu gungun sojoji suka sanar da hambarar da shi, suka kuma rufe iyakokin kasar tare da ayyana dokar ta-baci yayin da suka sanar da kafa gwamnatin mulkin soja.
Wannan dai shi ne karo na biyar da sojoji suka yi juyin mulki tun bayan samun ‘yancin kai a shekarar 1960.

Kafin juyin mulkin, a baya kasar Nijar ta sha juyin mulkin soji har sau hudu tun bayan samun ‘yancin kai daga Faransa a 1960, inda na karshe ya kasance a shekarar 2010. A tsakanin, an kuma yi yunkurin juyin mulki da dama, wanda na baya-bayan nan shi ne a shekarar 2021, lokacin da ‘yan adawar soji suka yi yunkurin kwace fadar shugaban kasar kwanaki biyu gabanin rantsar da zababben shugaban kasa Bazoum, wanda shi ne shugaban kasar na farko da ya karbi mulki daga hannun zababben shugaban kasa ta hanyar dimokuradiyya.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karbi ‘Yan Nijeriya 108 Da Suka Makale A Nijar
  • Sin Na Adawa Da Kutse Ta Intanet

Bayan juyin mulkin, Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) karkashin shugabancin shugaban kasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ta kakaba wa kasar takunkumin karya tattalin arzki inda aka umarci janye harkokin kasuwanci da tallafi ga kasar.

Tuni Nijeriya ta katse wutar lantarki da take ba Nijar, haka kuma an rufe iyakokin kasar ta yadda kayan abinci da na rayuwar yau da kullum suka daina zirga-zirga.

Wannan ya jefa rayuwar al’ummar kasar cikin matsanancin wahala musamman ganin kasar ta dogara ne a bangarori da dama da abububwa da ake shigowa da su daga kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

LEADERSHIP Hausa, ta tattauna da wani dan asalin kasar da ke Lele Birnin Ader a Jihar Tawa, Malam Yusuf Buzu, inda ya yi bayanin cewa abubuwa sun tabarbare ba kamar yadda gwamnatin sojan ke kokarin nuna wa duniya ba, karfin hali ne kawai suke yi amma al’umma na cikin tasku.

“Muna nan, sai addu’a, rayuwa sai hamdala, gaskiya akwai damuwa sosai game da mulkin sojoji, wallahi mu talakawa muna cikin kuncin rayuwa, da wanda ya yi murnar juyin mulkin da wanda bai yi ba dukkanmu muna cikin wahala, don gaskiya, Shugaban Soji Chani Abdurahaman ba shi da kwarewar tafiyar da kasa.

“A halin yanzu muna fuskantar tsadar abinci ga shi babu kudade a hannun al’umma, an rufe Babban Bankin Kasa, ba abin da ke shigowa Nijar, ga shi kuma masu kudi ba sa jin tsoron Allah, talaka ne kawai yake shan wahala, kuma ‘yan bindiga na cin karensu babu babbaka a kauyuka suna kashe na kashewa suna kama na kamawa, sai wanda Allah ya kare.”

Malam Yusuf Buzu ya ci gaba da cewa, “Nijar na hali mara dadi, abinci ya yi wuya, ka samu kudi amma ba su da darajar da za ka yi wani abu da su. Ana sayar da Shinkafa a kan jika goma shadaya zuwa da rabi kafin juyin mulkin amma a halin yanzu farashin ya kai jikka goma sha bakwai cikin birnin Tawa, a kauye kuma ya kai jikka goma sha tara a wasu kauyukan ma har jikka ashirin yake saboda tsadar kudin mota da ake zirga-zirgar safarar shinkafar.”
Ya kuma ce, wasu ‘yan kasuwar kasar ba su jin tsoron Allah, “duk da cewa, abubuwa da ake ci zuwa yanzu nasu ne wadanda suka ajiye, don yau (ranar Laraba) kusan kwanaki fiye da dari da ashirin ke nan babu kayan da ake shigo da shi cikin kasa saboda rufe iyakoki sakamakon juyin mulki, amma kuma sun tsauwala farashi.”

Sai dai kuma, ya yaba wa wasu daga cikin ‘yan kasuwa da masu kudi wadanda suke tausaya wa al’umma, yana mai cewa, “kai! duniya ta zo karshe, kowa kansa ya sani, mutane daga kansu yaransu, matansu sai daidaiku, kasan ba a yi wa al’umma jam’i, har gobe akwai mutanen kirki, ni kaina nakan wuni ban ci abinci ba a farkon mulkin sojan nan, amma kuma na samu taimako daga mutanen kirki.”

A halin yanzu dai, in ji Malam Yusuf, duk wani dan Nijar abin da ke gabansa shi ne neman samun saukin rayuwa, “a samu samu abinci a cikin sauki a kuma samu zaman lafiya har da ma dukkan ‘yan jam’iyyar PNDS Tarayya wanda juyin mulkin bai yi musu dadi ba, da farko talakawa sun nuna jin dadi amma yanzu murna ta koma ciki.

“Wannan halin da aka shiga ya sanya wasu ke tunani ko Bazoum zai dawo kan karagar mulki duk da cewa, dole shugaba ya yi makiya da masoya in yana mulki amma al’umma Nijjar sun ga ayyukan alhairin da ya yi na tsawon shekara biyu da wata 6”, in ji shi.

Ya kuma ce, babban abin da talaka ke nema daga dukkan masu mulki shi ne zaman lafiya walwala da abin da za a ci cikin adalci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Muhammed Danasabe, Ya Rasu

Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Muhammed Danasabe, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.