ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Ake Ciki Bayan Wata Hudu Da Juyin Mulkin Nijar

•Murnar Wasu Ta Koma Ciki – Yusuf Buzu

by Bello Hamza
3 years ago
Nijar

A ranar 26 ga watan Yulin shekara ta 2023, sojoji daga masu gadin fadar shugaban kasar, Nijar suka tsare shugaba Mohamed Bazoum, yayin da wasu gungun sojoji suka sanar da hambarar da shi, suka kuma rufe iyakokin kasar tare da ayyana dokar ta-baci yayin da suka sanar da kafa gwamnatin mulkin soja.
Wannan dai shi ne karo na biyar da sojoji suka yi juyin mulki tun bayan samun ‘yancin kai a shekarar 1960.

Kafin juyin mulkin, a baya kasar Nijar ta sha juyin mulkin soji har sau hudu tun bayan samun ‘yancin kai daga Faransa a 1960, inda na karshe ya kasance a shekarar 2010. A tsakanin, an kuma yi yunkurin juyin mulki da dama, wanda na baya-bayan nan shi ne a shekarar 2021, lokacin da ‘yan adawar soji suka yi yunkurin kwace fadar shugaban kasar kwanaki biyu gabanin rantsar da zababben shugaban kasa Bazoum, wanda shi ne shugaban kasar na farko da ya karbi mulki daga hannun zababben shugaban kasa ta hanyar dimokuradiyya.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karbi ‘Yan Nijeriya 108 Da Suka Makale A Nijar
  • Sin Na Adawa Da Kutse Ta Intanet

Bayan juyin mulkin, Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) karkashin shugabancin shugaban kasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ta kakaba wa kasar takunkumin karya tattalin arzki inda aka umarci janye harkokin kasuwanci da tallafi ga kasar.

ADVERTISEMENT

Tuni Nijeriya ta katse wutar lantarki da take ba Nijar, haka kuma an rufe iyakokin kasar ta yadda kayan abinci da na rayuwar yau da kullum suka daina zirga-zirga.

Wannan ya jefa rayuwar al’ummar kasar cikin matsanancin wahala musamman ganin kasar ta dogara ne a bangarori da dama da abububwa da ake shigowa da su daga kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

LEADERSHIP Hausa, ta tattauna da wani dan asalin kasar da ke Lele Birnin Ader a Jihar Tawa, Malam Yusuf Buzu, inda ya yi bayanin cewa abubuwa sun tabarbare ba kamar yadda gwamnatin sojan ke kokarin nuna wa duniya ba, karfin hali ne kawai suke yi amma al’umma na cikin tasku.

“Muna nan, sai addu’a, rayuwa sai hamdala, gaskiya akwai damuwa sosai game da mulkin sojoji, wallahi mu talakawa muna cikin kuncin rayuwa, da wanda ya yi murnar juyin mulkin da wanda bai yi ba dukkanmu muna cikin wahala, don gaskiya, Shugaban Soji Chani Abdurahaman ba shi da kwarewar tafiyar da kasa.

“A halin yanzu muna fuskantar tsadar abinci ga shi babu kudade a hannun al’umma, an rufe Babban Bankin Kasa, ba abin da ke shigowa Nijar, ga shi kuma masu kudi ba sa jin tsoron Allah, talaka ne kawai yake shan wahala, kuma ‘yan bindiga na cin karensu babu babbaka a kauyuka suna kashe na kashewa suna kama na kamawa, sai wanda Allah ya kare.”

Malam Yusuf Buzu ya ci gaba da cewa, “Nijar na hali mara dadi, abinci ya yi wuya, ka samu kudi amma ba su da darajar da za ka yi wani abu da su. Ana sayar da Shinkafa a kan jika goma shadaya zuwa da rabi kafin juyin mulkin amma a halin yanzu farashin ya kai jikka goma sha bakwai cikin birnin Tawa, a kauye kuma ya kai jikka goma sha tara a wasu kauyukan ma har jikka ashirin yake saboda tsadar kudin mota da ake zirga-zirgar safarar shinkafar.”
Ya kuma ce, wasu ‘yan kasuwar kasar ba su jin tsoron Allah, “duk da cewa, abubuwa da ake ci zuwa yanzu nasu ne wadanda suka ajiye, don yau (ranar Laraba) kusan kwanaki fiye da dari da ashirin ke nan babu kayan da ake shigo da shi cikin kasa saboda rufe iyakoki sakamakon juyin mulki, amma kuma sun tsauwala farashi.”

Sai dai kuma, ya yaba wa wasu daga cikin ‘yan kasuwa da masu kudi wadanda suke tausaya wa al’umma, yana mai cewa, “kai! duniya ta zo karshe, kowa kansa ya sani, mutane daga kansu yaransu, matansu sai daidaiku, kasan ba a yi wa al’umma jam’i, har gobe akwai mutanen kirki, ni kaina nakan wuni ban ci abinci ba a farkon mulkin sojan nan, amma kuma na samu taimako daga mutanen kirki.”

A halin yanzu dai, in ji Malam Yusuf, duk wani dan Nijar abin da ke gabansa shi ne neman samun saukin rayuwa, “a samu samu abinci a cikin sauki a kuma samu zaman lafiya har da ma dukkan ‘yan jam’iyyar PNDS Tarayya wanda juyin mulkin bai yi musu dadi ba, da farko talakawa sun nuna jin dadi amma yanzu murna ta koma ciki.

“Wannan halin da aka shiga ya sanya wasu ke tunani ko Bazoum zai dawo kan karagar mulki duk da cewa, dole shugaba ya yi makiya da masoya in yana mulki amma al’umma Nijjar sun ga ayyukan alhairin da ya yi na tsawon shekara biyu da wata 6”, in ji shi.

Ya kuma ce, babban abin da talaka ke nema daga dukkan masu mulki shi ne zaman lafiya walwala da abin da za a ci cikin adalci.

nijar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Muhammed Danasabe, Ya Rasu

Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Muhammed Danasabe, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.