• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Han Zheng Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Ci Gaba Da Bin Tsarin Bangarori Daban-daban Da Kyautata Tsarin Shugabancin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Han Zheng Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Ci Gaba Da Bin Tsarin Bangarori Daban-daban Da Kyautata Tsarin Shugabancin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin shugaban kasar Sin, Han Zheng, a cikin jawabinsa a zauren taron MDD a jiya Alhamis, ya yi kira ga kasashen duniya da su tsaya tsayin daka kan ra’ayin bangarori daban-daban, da kyautata tsarin tafiyar da harkokin duniya.

Da yake jawabi a babbar muhawara a gun babban taron MDD karo na 78, Han ya ce kamata ya yi kasashe mambobin MDD su tabbatar da daidaito da adalci, da kiyaye zaman lafiya da tsaro, da tabbatar da moriyar juna, da samar da nasara da ci gaba ga kowa da kowa, da hada kai, da ciyar da wayewar bil Adama gaba, kuma su kasance masu gaskiya ga tsarin hadin gwiwa da inganta tsarin shugabancin duniya.

  • Sin Tana Nacewa Ga Matsayin Ta A Rukunin Kasashen “Global South”

Da yake karin haske game da batun ci gaba, Han ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa a fannin shirin shawarar ziri daya da hanya daya da kuma ajandar ci gaba mai dorewa ta 2030, inda ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da ba da gudummawa wajen gina al’ummar duniya baki daya. Ya kamata kasashe da al’ummomi mabambanta su yi rayuwar ci gaba tare ta hanyar mutunta juna, su yi amfani da karfin juna wajen samun ci gaba, da cimma nasara ta hanyar hadin gwiwa.

Dangane da batun kare hakkin bil Adama, mataimakin shugaban kasar ya ce, ya kamata kasashen duniya su ciyar da harkokin kare hakkin bil Adama na kasa da kasa gaba ta hanyar hadin gwiwa, tare da yin adawa da siyasantar da batun hakkin bil Adama.

Han ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne, ya kamata duniya ta tsaya tsayin daka wajen adawa da amfani da hakkin dan Adam da dimokuradiyya a matsayin wani makamin siyasa wajen tsoma baki cikin harkokin wasu kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Ya kuma bukaci kasashen duniya da su karfafa wakilci da muryar kasashe masu tasowa da tabbatar da gudanar da shugabancin duniya cikin adalci da daidaito. (Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da A Aiwatar Da Matakan Bunkasa Kudaden Shigar Manoma Da Kara Kyautata Rayuwarsu

Next Post

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

Related

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

2 hours ago
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
Daga Birnin Sin

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

3 hours ago
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

20 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

21 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

22 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

23 hours ago
Next Post
Kotu

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.