A yau Jumma’a 30 ga wata, mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya halarci bikin bude taron tattaunawa karo na hudu kan musaya da koyi da juna a tsakanin al’ummomi ta fannin wayewar kansu a birnin Dunhuang na lardin Gansu, inda ya gabatar da jawabi.
Han Zheng ya ce, a cikin duniyar yau wacce makomar dukkan kasashe ke da alaka ta kut-da-kut, tabbatar da musaya da koyi da juna a tsakanin al’ummomi daban-daban ta fannin wayewar kansu zai taimaka wajen samun ci gaban bil’adama, tare da karfafa samun wadata da ci gaban duniya.
- Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
- Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Haka nan ya ce, a matsayin sabon salo na wayewar dan Adam, zamanantarwa mai sigar musamman ta kasar Sin ta yi koyi da sauran al’adun wayewar kai, kuma ta bayar da gudummawar hikima ta musamman ga ci gaban wayewar duniya.
A nasu bangaren, mai magana da yawun majalisar dokokin kasar Botswana Dithapelo Keorapetse, da mataimakin shugaban majalisar dokokin kasar Laos Sommad Pholsena, da tsohuwar shugabar kasar Nepal Misis Bidya Devi Bhandari, da sauran manyan kusoshin kasashen waje, sun bayyana cewa, kasar Sin ta samar da kwanciyar hankali da tabbaci ga duniya ta hanyar ci gaban da ta samu.
Sun kara da cewa, ta hanyar raya ruhin hanyar siliki da zurfafa ci gaban shawarar ziri daya da hanya daya, kasar Sin ta ba da goyon baya mai karfi ga bunkasar tattalin arziki da zamantakewa na kasashe masu tasowa da dama. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp