ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
Ingila

Matashin ɗan wasa Djed Spence ya zama zakaran gwajin dafi a matsayin Musulmi na farko da ya taɓa buga wa babbar tawagar ƴ anwasan Ingila wasan ƙwallon ƙafa a tarihin ƙasar.

Ɗanwasan bayan na ƙungiyar Tottenham ya buga wa tawagar ƴ an ƙasa da shekara 21 wasa sau shida, amma wannan ne karon farko da aka kira shi babbar tawagar da ta buga wasannin neman shiga gasar Kofin Duniya ta 2026.

Duk da cewa hukumar ƙwallon ƙafa ta Ingila ba ta adana bayanan addinin ƴ anwasanta, an fahimci cewa Spence zai iya zama Musulmi na farko da ya buga mata wasa Djed Spence ya ce abin alheri ne abin murna. Domin ya rasa ma kalaman da zai bayyana irin farin cikin da ya shiga lokacin da aka gayyace shi domin ya je ya wakilci ƙasar Ingila.

ADVERTISEMENT
  • Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
  • Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

“Ina yawan yin addu’a. Ina gode wa Allah a lokutan da nake cikin ƙunci.

Na yi imanin cewa Allah yana tare da ni a kodayaushe. Wannan muhimmin abu ne a wurina, da addinina.” In ji Djed Spence.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

Tottenham ta tura ɗanƙwallon wasan aro har sau uku zuwa ƙungiyoyin

Rennes, da Leeds, da Genoa a baya kuma a sakamakon haka ɗan wasan ya samu ƙwarewa da gogewa sosai.

Spence ya ce ba ya jin wani ƙarin nauyi saboda addininsa, amma yana fatan rawar da zai taka a tawagar za ta ƙarfafa wa sauran ƴ anwasa masu zuwa gwiwa domin cika burikansu.

Kafin 15 ga watan Disamba na shekarar da ta gabata, minti 64 kacal Spence ya buga a gasar Premier League a kakar 2004 zuwa 2025. Bayan haka ne kuma ya buga minti 90 sau 19 cikin wasanni 22 da ya buga wa Tottenham.

Sauyin da ya samu mai girma ne sosai. Da farko, tsohon mai horarwa Ange Postecoglou bai ma saka shi cikin tawagar ƙungiyar da ta buga gasar zakarun Turai ta Europa ba har sai da aka kai zagayen ƴ an 16 kafin ya buga minti 180 a wasan da suka doke AZ Alkamaar.

Sai kuma lokacin da ya shiga daga benci wasan ƙarshe da Tottenham ta doke Manchester United domin ɗaukar kofi karon farko cikin shekara 17, wanda ya ba su damar zuwa gasar Champions League. Bayan buga wa Tottenham kowane minti a kakar wasa ta bana, Spence ya samu kira daga mai horarwa Thomas Tuchel, kociyan tawagar Ingila wanda ake sa ran zai jagorancin ƙasar zuwa gasar cin kofin duniya na 2026 da za a buga a ƙasashen Amurka da Canada da kuma Meɗico.

Ɗan wasan ya ce “Tabbas abu ne muhimmi mutum ya samu damar buga wa Ingila wasa kuma kociyan tawagar ya tarɓe ni da kyau, kowa ya ba ni kyakkyawar tarɓa yadda ya kamata.

A watan Maris na shekarar 2022 ne ya fara buga wa ƴ an 21 wasa. A lokacin mai koyar da yanwasan Lee Carsley ya so ya gayyaci Spence gasar European Championship ta ƴ an ƙasa da shekara 21, amma sai rauni ya hana shi zuwa.

Lee Carsley ya taɓa faɗa wa shashen Hausa na BBC a farkon shekarar nan cewa: “Yana da ƙwarewa a fannoni; yadda yake jawo ƙwallo kuma ya yanka abokan hamayya, yake cin ƙwallon, yake tarewa. Ɗanwasa ne da ba shi da iyaka nan gaba.”

Kawo yanzu dai fatan da Djed Spence zai yi shi ne ya ci gaba da ƙoƙari har zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana domin hakan ne kawai zai sa kociyan tawagar ta Ingila Thomas Tuchel ya gayyace shi zuwa gasar cin kofin duniya.

Ingila
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan
Wasanni

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026
Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan
Wasanni

Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan

June 15, 2026
Next Post
Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya - Jami’ar EAU

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.