• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

by Abubakar Abba
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya, ta kaddamar da shirye-shirye guda biyar; domin dakile karancin abinci tare da daidaita farashinsa a 2025.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci Abubakar Kyari ne, ya bayyana haka a taron manema labarai a Abuja.

  • Faduwar Darajar Naira Ya Haifar Da Raguwar Kayan Da Ake Shigowa Da Su Nijeriya
  • Sinawa Kimanin Miliyan 1.85 Za Su Rika Zuwa Yawon Bude Ido a Ketare Kullum Lokacin Hutun Bikin Bazara

Inda ya bayyana cewa, gwamnatin ta mayar da hankali wajen ganin an kara bunkasa noma da kuma magance wa manoman kalubalen da suke fuskanta na gaza noman wadataccen amfanin gona.

Kyari ya yi nuni da cewa, dogaro kadai a kan kasafin kudi, bai zai iya wadatar da wannan fanni na noma ba.

Wadannan shirye-shiye biyar sun hada da:

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1- Gabatar Da Noman Alkama A Kakar Damina: Kyari ya ce, bisa kari da ci gaba da ake yi na shirin noman Alkama na rani a wasu jihohin kasar, za kuma a rungumi noman Alkama na damina, musamman a Jihohin Kuros Riba, Filato da Taraba.

“Wannan ne karo na farko da jihohin da ke Kudancin Kasar nan, za su bi sahun jihohi sha biyar da ake noman Alkamar”, in ji Kyari.

Sannan ya sanar da cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a shirin noman Alkamar na rani kashi na daya, ya kare a ranar 27 ga watan Disambar 2024.

“A karkashin shirin, mun taimaka da hektar noman Alkama 150,000, wanda hakan ya nuna cewa, manomanta 300,000 ne suka amfana da wannan hekta”, in ji Ministan.

Kyari ya kara da cewa, an kuma sayarwa da manomanta Iri kan farashi mai sauki, wanda aka yi masu ragi daga kashi 25 zuwa kashi 75.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma sayarwa da manoman takin zamani a kan farashi mai sauki, wanda ya kasance a kan  kashi 50 cikin 100.

A 2024, Kyari ya bayyana cewa, gwamnatin a karkashin shirin bayar da daukin noma na kasa, wato na tura wa manoma kudi ta hanyar amfani da manhajar zamani (NAGS-AP), manoman rani 400,000 ne gwamnatin ta taimakawa daga 2024 zuwa 2025.

2- Kwangilar Shigo Da Taraktocin Noma 2,000 Daga Kamfanin Belarus:

Kyari ya bayyana cewa, tuni wadannan taraktoci sun fara shigowa cikin wannan kasa, ta hanyar tashar jiragen ruwa da ke Legas, inda ya ce, za a raba wa manoman taraktocin ne da nufin kara bunkasa noman Tumatir a yankunan Kudu Maso Gabas da kuma na Kudu Maso Yamma.

Ya ce, taraktocin, a daya daga cikin yunkurin gwamnatin na karfafa wa manoman yin noman zamani.

3- Gyara Tsarin Bayar Da Kudin Rancen Yin Noma Na Bankin Aikin Noma (BoA):

Kyari ya sanar da shiry-shiyen gyara tsarin bayar da rance kudin yin noma na Bankin Aikin Noma, inda ya ce, Bankin wanda ke da rassa a mazabu 109 na kasar nan, za a saita shi don ya rika bayar da rance ga kanannan manoma.

A cewarsa, jawo abokan hadaka kamar irin su, Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), hakan zai taimaka wajen samar da damar samun kudade,

4- Kara Inganta Noma Da Kayan Aiki Na Zamani:

Kyari ya bayyana cewa, wannan na daya daga cikin burin Shugaba  Tinubu, na samar da taraktocin noma ga manoma.

5- Magance Asarar Da Manoma Ke Yi Bayan Girbe Amfanin Gona:

Kyari ya sanar da cewa, za a samar da shiye-shirye tare da tanadin  guraren adana amfanin gona da aka girbe, musammna domin magance asarar da manoman ke yi, da ta kai ta kimanin Naira tiriliyan 3.5, inda ya ce,  wannan matakin na daga cikin burin da Tinubu ke son cimma a  2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbincigwamnatiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Next Post

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 day ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.