• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

by Abubakar Abba
9 months ago
Hanyoyi

Gwamnatin tarayya, ta kaddamar da shirye-shirye guda biyar; domin dakile karancin abinci tare da daidaita farashinsa a 2025.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci Abubakar Kyari ne, ya bayyana haka a taron manema labarai a Abuja.

  • Faduwar Darajar Naira Ya Haifar Da Raguwar Kayan Da Ake Shigowa Da Su Nijeriya
  • Sinawa Kimanin Miliyan 1.85 Za Su Rika Zuwa Yawon Bude Ido a Ketare Kullum Lokacin Hutun Bikin Bazara

Inda ya bayyana cewa, gwamnatin ta mayar da hankali wajen ganin an kara bunkasa noma da kuma magance wa manoman kalubalen da suke fuskanta na gaza noman wadataccen amfanin gona.

Kyari ya yi nuni da cewa, dogaro kadai a kan kasafin kudi, bai zai iya wadatar da wannan fanni na noma ba.

Wadannan shirye-shiye biyar sun hada da:

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

1- Gabatar Da Noman Alkama A Kakar Damina: Kyari ya ce, bisa kari da ci gaba da ake yi na shirin noman Alkama na rani a wasu jihohin kasar, za kuma a rungumi noman Alkama na damina, musamman a Jihohin Kuros Riba, Filato da Taraba.

“Wannan ne karo na farko da jihohin da ke Kudancin Kasar nan, za su bi sahun jihohi sha biyar da ake noman Alkamar”, in ji Kyari.

Sannan ya sanar da cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a shirin noman Alkamar na rani kashi na daya, ya kare a ranar 27 ga watan Disambar 2024.

“A karkashin shirin, mun taimaka da hektar noman Alkama 150,000, wanda hakan ya nuna cewa, manomanta 300,000 ne suka amfana da wannan hekta”, in ji Ministan.

Kyari ya kara da cewa, an kuma sayarwa da manomanta Iri kan farashi mai sauki, wanda aka yi masu ragi daga kashi 25 zuwa kashi 75.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma sayarwa da manoman takin zamani a kan farashi mai sauki, wanda ya kasance a kan  kashi 50 cikin 100.

A 2024, Kyari ya bayyana cewa, gwamnatin a karkashin shirin bayar da daukin noma na kasa, wato na tura wa manoma kudi ta hanyar amfani da manhajar zamani (NAGS-AP), manoman rani 400,000 ne gwamnatin ta taimakawa daga 2024 zuwa 2025.

2- Kwangilar Shigo Da Taraktocin Noma 2,000 Daga Kamfanin Belarus:

Kyari ya bayyana cewa, tuni wadannan taraktoci sun fara shigowa cikin wannan kasa, ta hanyar tashar jiragen ruwa da ke Legas, inda ya ce, za a raba wa manoman taraktocin ne da nufin kara bunkasa noman Tumatir a yankunan Kudu Maso Gabas da kuma na Kudu Maso Yamma.

Ya ce, taraktocin, a daya daga cikin yunkurin gwamnatin na karfafa wa manoman yin noman zamani.

3- Gyara Tsarin Bayar Da Kudin Rancen Yin Noma Na Bankin Aikin Noma (BoA):

Kyari ya sanar da shiry-shiyen gyara tsarin bayar da rance kudin yin noma na Bankin Aikin Noma, inda ya ce, Bankin wanda ke da rassa a mazabu 109 na kasar nan, za a saita shi don ya rika bayar da rance ga kanannan manoma.

A cewarsa, jawo abokan hadaka kamar irin su, Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), hakan zai taimaka wajen samar da damar samun kudade,

4- Kara Inganta Noma Da Kayan Aiki Na Zamani:

Kyari ya bayyana cewa, wannan na daya daga cikin burin Shugaba  Tinubu, na samar da taraktocin noma ga manoma.

5- Magance Asarar Da Manoma Ke Yi Bayan Girbe Amfanin Gona:

Kyari ya sanar da cewa, za a samar da shiye-shirye tare da tanadin  guraren adana amfanin gona da aka girbe, musammna domin magance asarar da manoman ke yi, da ta kai ta kimanin Naira tiriliyan 3.5, inda ya ce,  wannan matakin na daga cikin burin da Tinubu ke son cimma a  2025.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.