• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

by Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya, ta kaddamar da shirye-shirye guda biyar; domin dakile karancin abinci tare da daidaita farashinsa a 2025.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci Abubakar Kyari ne, ya bayyana haka a taron manema labarai a Abuja.

  • Faduwar Darajar Naira Ya Haifar Da Raguwar Kayan Da Ake Shigowa Da Su Nijeriya
  • Sinawa Kimanin Miliyan 1.85 Za Su Rika Zuwa Yawon Bude Ido a Ketare Kullum Lokacin Hutun Bikin Bazara

Inda ya bayyana cewa, gwamnatin ta mayar da hankali wajen ganin an kara bunkasa noma da kuma magance wa manoman kalubalen da suke fuskanta na gaza noman wadataccen amfanin gona.

Kyari ya yi nuni da cewa, dogaro kadai a kan kasafin kudi, bai zai iya wadatar da wannan fanni na noma ba.

Wadannan shirye-shiye biyar sun hada da:

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

1- Gabatar Da Noman Alkama A Kakar Damina: Kyari ya ce, bisa kari da ci gaba da ake yi na shirin noman Alkama na rani a wasu jihohin kasar, za kuma a rungumi noman Alkama na damina, musamman a Jihohin Kuros Riba, Filato da Taraba.

“Wannan ne karo na farko da jihohin da ke Kudancin Kasar nan, za su bi sahun jihohi sha biyar da ake noman Alkamar”, in ji Kyari.

Sannan ya sanar da cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a shirin noman Alkamar na rani kashi na daya, ya kare a ranar 27 ga watan Disambar 2024.

“A karkashin shirin, mun taimaka da hektar noman Alkama 150,000, wanda hakan ya nuna cewa, manomanta 300,000 ne suka amfana da wannan hekta”, in ji Ministan.

Kyari ya kara da cewa, an kuma sayarwa da manomanta Iri kan farashi mai sauki, wanda aka yi masu ragi daga kashi 25 zuwa kashi 75.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma sayarwa da manoman takin zamani a kan farashi mai sauki, wanda ya kasance a kan  kashi 50 cikin 100.

A 2024, Kyari ya bayyana cewa, gwamnatin a karkashin shirin bayar da daukin noma na kasa, wato na tura wa manoma kudi ta hanyar amfani da manhajar zamani (NAGS-AP), manoman rani 400,000 ne gwamnatin ta taimakawa daga 2024 zuwa 2025.

2- Kwangilar Shigo Da Taraktocin Noma 2,000 Daga Kamfanin Belarus:

Kyari ya bayyana cewa, tuni wadannan taraktoci sun fara shigowa cikin wannan kasa, ta hanyar tashar jiragen ruwa da ke Legas, inda ya ce, za a raba wa manoman taraktocin ne da nufin kara bunkasa noman Tumatir a yankunan Kudu Maso Gabas da kuma na Kudu Maso Yamma.

Ya ce, taraktocin, a daya daga cikin yunkurin gwamnatin na karfafa wa manoman yin noman zamani.

3- Gyara Tsarin Bayar Da Kudin Rancen Yin Noma Na Bankin Aikin Noma (BoA):

Kyari ya sanar da shiry-shiyen gyara tsarin bayar da rance kudin yin noma na Bankin Aikin Noma, inda ya ce, Bankin wanda ke da rassa a mazabu 109 na kasar nan, za a saita shi don ya rika bayar da rance ga kanannan manoma.

A cewarsa, jawo abokan hadaka kamar irin su, Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), hakan zai taimaka wajen samar da damar samun kudade,

4- Kara Inganta Noma Da Kayan Aiki Na Zamani:

Kyari ya bayyana cewa, wannan na daya daga cikin burin Shugaba  Tinubu, na samar da taraktocin noma ga manoma.

5- Magance Asarar Da Manoma Ke Yi Bayan Girbe Amfanin Gona:

Kyari ya sanar da cewa, za a samar da shiye-shirye tare da tanadin  guraren adana amfanin gona da aka girbe, musammna domin magance asarar da manoman ke yi, da ta kai ta kimanin Naira tiriliyan 3.5, inda ya ce,  wannan matakin na daga cikin burin da Tinubu ke son cimma a  2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbincigwamnatiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Next Post

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.