ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

by Abubakar Abba
2 years ago
Hanyoyi

Gwamnatin tarayya, ta kaddamar da shirye-shirye guda biyar; domin dakile karancin abinci tare da daidaita farashinsa a 2025.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci Abubakar Kyari ne, ya bayyana haka a taron manema labarai a Abuja.

  • Faduwar Darajar Naira Ya Haifar Da Raguwar Kayan Da Ake Shigowa Da Su Nijeriya
  • Sinawa Kimanin Miliyan 1.85 Za Su Rika Zuwa Yawon Bude Ido a Ketare Kullum Lokacin Hutun Bikin Bazara

Inda ya bayyana cewa, gwamnatin ta mayar da hankali wajen ganin an kara bunkasa noma da kuma magance wa manoman kalubalen da suke fuskanta na gaza noman wadataccen amfanin gona.

ADVERTISEMENT

Kyari ya yi nuni da cewa, dogaro kadai a kan kasafin kudi, bai zai iya wadatar da wannan fanni na noma ba.

Wadannan shirye-shiye biyar sun hada da:

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

1- Gabatar Da Noman Alkama A Kakar Damina: Kyari ya ce, bisa kari da ci gaba da ake yi na shirin noman Alkama na rani a wasu jihohin kasar, za kuma a rungumi noman Alkama na damina, musamman a Jihohin Kuros Riba, Filato da Taraba.

“Wannan ne karo na farko da jihohin da ke Kudancin Kasar nan, za su bi sahun jihohi sha biyar da ake noman Alkamar”, in ji Kyari.

Sannan ya sanar da cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a shirin noman Alkamar na rani kashi na daya, ya kare a ranar 27 ga watan Disambar 2024.

“A karkashin shirin, mun taimaka da hektar noman Alkama 150,000, wanda hakan ya nuna cewa, manomanta 300,000 ne suka amfana da wannan hekta”, in ji Ministan.

Kyari ya kara da cewa, an kuma sayarwa da manomanta Iri kan farashi mai sauki, wanda aka yi masu ragi daga kashi 25 zuwa kashi 75.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma sayarwa da manoman takin zamani a kan farashi mai sauki, wanda ya kasance a kan  kashi 50 cikin 100.

A 2024, Kyari ya bayyana cewa, gwamnatin a karkashin shirin bayar da daukin noma na kasa, wato na tura wa manoma kudi ta hanyar amfani da manhajar zamani (NAGS-AP), manoman rani 400,000 ne gwamnatin ta taimakawa daga 2024 zuwa 2025.

2- Kwangilar Shigo Da Taraktocin Noma 2,000 Daga Kamfanin Belarus:

Kyari ya bayyana cewa, tuni wadannan taraktoci sun fara shigowa cikin wannan kasa, ta hanyar tashar jiragen ruwa da ke Legas, inda ya ce, za a raba wa manoman taraktocin ne da nufin kara bunkasa noman Tumatir a yankunan Kudu Maso Gabas da kuma na Kudu Maso Yamma.

Ya ce, taraktocin, a daya daga cikin yunkurin gwamnatin na karfafa wa manoman yin noman zamani.

3- Gyara Tsarin Bayar Da Kudin Rancen Yin Noma Na Bankin Aikin Noma (BoA):

Kyari ya sanar da shiry-shiyen gyara tsarin bayar da rance kudin yin noma na Bankin Aikin Noma, inda ya ce, Bankin wanda ke da rassa a mazabu 109 na kasar nan, za a saita shi don ya rika bayar da rance ga kanannan manoma.

A cewarsa, jawo abokan hadaka kamar irin su, Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), hakan zai taimaka wajen samar da damar samun kudade,

4- Kara Inganta Noma Da Kayan Aiki Na Zamani:

Kyari ya bayyana cewa, wannan na daya daga cikin burin Shugaba  Tinubu, na samar da taraktocin noma ga manoma.

5- Magance Asarar Da Manoma Ke Yi Bayan Girbe Amfanin Gona:

Kyari ya sanar da cewa, za a samar da shiye-shirye tare da tanadin  guraren adana amfanin gona da aka girbe, musammna domin magance asarar da manoman ke yi, da ta kai ta kimanin Naira tiriliyan 3.5, inda ya ce,  wannan matakin na daga cikin burin da Tinubu ke son cimma a  2025.

Hanyoyi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Kemis Da Kama Mutum Biyu Masu Sayar Da Jabun Magunguna A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.