• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

by Rabi'u Ali Indabawa
13 hours ago
Noma

Shugaban Kwamitin Bincike a cibiyar binciken aikin noma IAR na, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, Farfesa Rabiu Adamu, ya ce hanyoyin noma na gargajiya ba za su iya samar da biyan bukatar abinci a Nijeriya ba, don haka ba mai dorewa ba ne, musamman saboda yawaitar jama’a da raguwar filayen noma.

Ya ce Nijeriya, wadda ita ce kasa mafi yawan jama’a a Afirka, tana samar da tan miliyan 12.4 na masara, alhali bukatar kasa ita ce tan miliyan 18.

  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Domin magance gibin, farfesan ya ce gwamnati ta amince a kawo sabon iri na masara mai yawan amfanarwa, mai jure fari da kwari.

Ya ce, “Nijeriya har yanzu na bukatar ta inganta yawan amfanin gona a kowane fadin fili. A halin yanzu, a kan hekta daya, ana samun kasa da tan 3, don haka akwai bukatar a inganta wannan, domin kaucewa gurbacewar kasa ta hanyar fadada birane, gina hanyoyi da sauran abubuwa kamar hamada sun rika raguwa da filayen noma.

Don kara yawan amfanin gona, ana bukatar irin shuka mai yawan amfanarwa, wacce ba ta bukatar magungunan kashe ciyawa ko kwari, ko ma takin zamani,” in ji Adamu.

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

Dangane da fargaba game da karancin abinci na amfanin gona da aka canza jinsinsu (GMOs), farfesan ya ce domin tabbatar da lafiyar abinci da kare lafiyar jama’a, dole ne kowace iri da za ta shigo kasar ta bi matakan doka da ka’idoji da ke tabbatar da cewa tana da aminci. Ya ce, dokokin da ake amfani da su wajen kula da GMOs ma sun fi tsauri fiye da na amfanin gona na gargajiya saboda an kara musu sinadaran halittu (genetic materials).

“Kafin a saki kowane irin amfanin gona domin a fara amfani da shi a kasuwanci, dole ne ta bi diddigin binciken halittu da sinadaran gina jiki sosai. Bayanai da ake da su a halin yanzu sun nuna cewa amfanin gona na GMO suna da lafiya, bisa sama da bincike 200 da aka gudanar a Turai, Amurka, Latin Amurka da wasu kasashen Afirka.

Shi ya sa aka amince a ci su, domin sun cika sharudan tsaro. Babu wani rahoto daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ko kuma Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) da ya nuna cewa amfanin gona ko abincin da aka sarrafa ta hanyar ilmin kwayoyin halitta (GMO) na da illa ga mutane ko dabbobi.

A halin yanzu akwai amfanin gona irin su masara, tumatir, shinkafa, waken suya da gwanda da aka sarrafa ta hanyar GMO a kasuwa. Babu wani tabbacin matsalar tsaro game da hakan.”

Adamu ya ce Nijeriya ba ta samar da isasshen abinci na gargajiya (organic) ba, sai dai amfanin gona na yau da kullum kamar sauran kasashe masu tasowa, inda manoma ke amfani da takin zamani, magungunan kashe kwari da sauran sinadarai.

Ya bayyana cewa amfanin gona na kwayoyin halitta (GM crops), an noman wasu daga cikinsu ne domin su iya jure matsalolin da manoma ke fuskanta a lokacin noman su, kamar kwari masu lalata shuka, irin su stem borer da kuma kwaron fall armyworm.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Next Post
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.