• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ina Fuskantar Matsala Saboda Shigowata Harkar Fim —Saratu Abubakar

by Bello Hamza
3 years ago
in Nishadi
0
Saratu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabuwar jaruma a masana’antar finafinai ta Kannywood, ta bayyana shigowar ta masana’antar da cewa lokacin ta ne ya yi don haka ba ta yi mamaki ba da ta kasance cikin wadanda a ke damawa da su a cikin harkar, saboda yadda ta dade ta na son ta yi tun ta na karama don haka sai a yanzu ne ta samu cikar burin ta na zama ‘yar fim.

Jarumar ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar mu da ita Inda take cewa, “Tsawon lokacin da na yi ina fatan na kasance ‘yar fim sai a yanzu na cika burina wanda a yanzu duk da ban dade da shigowa ba, don na fara ne a 2020 in da na fara fitowa a fim din ‘Hajiya Babba’ da ‘Ya’yan Mage’, kuma a yanzu ni ce jarumar fim din ‘Zo Mu Zauna’, kuma ina jin dadi sosai da hakan’.

  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Dangane da ko ta samu matsala daga gidan su a lokacin da ta shigo kuwa cewa ta yi, “Ai matsala sosai ma kuwa don har yanzu ina fuskantar matsalar, saboda ka san shi fim a nan kasar mu ta Hausa idan mutum ya na yi sai a rinka cewa shi dan iska ne.

To wannan ta sa har gida aka je a ke samun iyaye na ana cewa sun bar ni ina iskanci har abin ya yi musu yawa su ke ta mini magana, don haka sai nake fada musu cewa ni fa a rayuwa ta ba zan yi abin da bai dace ba, ni na san din sana’a ce kuma ita ta kawo ni, neman kudi nake yi, kuma ba wai zaman banza nake yi ba a Kano karatu nake yi sai kuma nake hadawa da fim saboda sana’a ce, don haka ba iskanci nake yi ba na dauke shi a matsayin sana’a da zan rinka yi ina rufawa kaina asiri, to haka dai suka yarda suka hakura tunda ya za su yi da ni, tunda ina cikin fim din na shiga dumu-dumu, kawai dai sai wani lokacin idan na je gida za a ce shikenan dai na shiga harkar fim ba zan yi aure ba.

Na Kano ce musu aure lokaci ne idan Allah ya kawo za a yi.”
Dangane da fim din da ta fito a matsayin Jaruma kuwa wato zo mu zauna cewa ta yi ‘Ina alfahari da fim din, domin shi ne ya fito da ni duniya ta san da ni kuma matsayin da aka ba ni na babbar Mace ya zo mini da bazata, saboda a matsayina na Budurwa da ban taba yin aure ba sai ga shi a fim na kasance matar aure har da babbar ‘ya da zan aurar da ita.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Wannan matsayin ya daga daraja ta sai na zo ina jin kaina kamar matar aure ka ga wannan ai daukaka ce, don haka a kullum ina alfahari da fim din ‘Zo Mu Zauna.”

A game da mu’amalarta da mutane kuwa cewa ta yi ta samu ce gaba sosai.”Domin duk lokacin da na je gida, sai ka ga duk wajen da na shiga a na ta zuwa wajena don ma ba ko’ina nake shiga ba saboda duk in da ka je za a ta kallon ka”.

A game da yadda mu’amalarta take kasancewa da masoyanta kuwa cewa ta yi abin ya na burge ta saboda “Duk in da na je a na zuwa a dauki hoto da ni kuma ina samun kyauta daga wajen masoyana sannan kuma idan na shiga cikin ‘yan fim mu kan zama kamar ‘yan’uwa don ba na gane ma ba a gida nake ba saboda an hadu an zama daya, haka a ke zama a yi wasa da dariya, don yau idan ba ni da lafiya na san wanda zan kira a cikin ‘yan fim ya tsaya a kaina.

Don haka muna zama ne kamar ‘yan uwan juna.”
Daga karshe ta yi kira ga jama’a da su daina yi wa ‘yan fim kallon ‘yan iska, saboda ba kowa ba ne dan iska, don akwai mutane nagari kamar kowacce harkar, da mutanen kirki da na banza, to haka ma harkar fim take. Inji Saratu Abubakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayani A Game Da Sabuwar Wayar iPhone 14 (Kimiyya)

Next Post

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

4 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.