ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ina Fuskantar Matsala Saboda Shigowata Harkar Fim —Saratu Abubakar

by Bello Hamza
4 years ago
Saratu

Sabuwar jaruma a masana’antar finafinai ta Kannywood, ta bayyana shigowar ta masana’antar da cewa lokacin ta ne ya yi don haka ba ta yi mamaki ba da ta kasance cikin wadanda a ke damawa da su a cikin harkar, saboda yadda ta dade ta na son ta yi tun ta na karama don haka sai a yanzu ne ta samu cikar burin ta na zama ‘yar fim.

Jarumar ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar mu da ita Inda take cewa, “Tsawon lokacin da na yi ina fatan na kasance ‘yar fim sai a yanzu na cika burina wanda a yanzu duk da ban dade da shigowa ba, don na fara ne a 2020 in da na fara fitowa a fim din ‘Hajiya Babba’ da ‘Ya’yan Mage’, kuma a yanzu ni ce jarumar fim din ‘Zo Mu Zauna’, kuma ina jin dadi sosai da hakan’.

  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Dangane da ko ta samu matsala daga gidan su a lokacin da ta shigo kuwa cewa ta yi, “Ai matsala sosai ma kuwa don har yanzu ina fuskantar matsalar, saboda ka san shi fim a nan kasar mu ta Hausa idan mutum ya na yi sai a rinka cewa shi dan iska ne.

ADVERTISEMENT

To wannan ta sa har gida aka je a ke samun iyaye na ana cewa sun bar ni ina iskanci har abin ya yi musu yawa su ke ta mini magana, don haka sai nake fada musu cewa ni fa a rayuwa ta ba zan yi abin da bai dace ba, ni na san din sana’a ce kuma ita ta kawo ni, neman kudi nake yi, kuma ba wai zaman banza nake yi ba a Kano karatu nake yi sai kuma nake hadawa da fim saboda sana’a ce, don haka ba iskanci nake yi ba na dauke shi a matsayin sana’a da zan rinka yi ina rufawa kaina asiri, to haka dai suka yarda suka hakura tunda ya za su yi da ni, tunda ina cikin fim din na shiga dumu-dumu, kawai dai sai wani lokacin idan na je gida za a ce shikenan dai na shiga harkar fim ba zan yi aure ba.

Na Kano ce musu aure lokaci ne idan Allah ya kawo za a yi.”
Dangane da fim din da ta fito a matsayin Jaruma kuwa wato zo mu zauna cewa ta yi ‘Ina alfahari da fim din, domin shi ne ya fito da ni duniya ta san da ni kuma matsayin da aka ba ni na babbar Mace ya zo mini da bazata, saboda a matsayina na Budurwa da ban taba yin aure ba sai ga shi a fim na kasance matar aure har da babbar ‘ya da zan aurar da ita.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Wannan matsayin ya daga daraja ta sai na zo ina jin kaina kamar matar aure ka ga wannan ai daukaka ce, don haka a kullum ina alfahari da fim din ‘Zo Mu Zauna.”

A game da mu’amalarta da mutane kuwa cewa ta yi ta samu ce gaba sosai.”Domin duk lokacin da na je gida, sai ka ga duk wajen da na shiga a na ta zuwa wajena don ma ba ko’ina nake shiga ba saboda duk in da ka je za a ta kallon ka”.

A game da yadda mu’amalarta take kasancewa da masoyanta kuwa cewa ta yi abin ya na burge ta saboda “Duk in da na je a na zuwa a dauki hoto da ni kuma ina samun kyauta daga wajen masoyana sannan kuma idan na shiga cikin ‘yan fim mu kan zama kamar ‘yan’uwa don ba na gane ma ba a gida nake ba saboda an hadu an zama daya, haka a ke zama a yi wasa da dariya, don yau idan ba ni da lafiya na san wanda zan kira a cikin ‘yan fim ya tsaya a kaina.

Don haka muna zama ne kamar ‘yan uwan juna.”
Daga karshe ta yi kira ga jama’a da su daina yi wa ‘yan fim kallon ‘yan iska, saboda ba kowa ba ne dan iska, don akwai mutane nagari kamar kowacce harkar, da mutanen kirki da na banza, to haka ma harkar fim take. Inji Saratu Abubakar.

Saratu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Abin Da Ya Kamata Ka Sani Kan Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Saratu
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Saratu

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Saratu

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.