• Leadership Hausa
Tuesday, February 7, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Nishadi

Har Yanzu Ina Fuskantar Matsala Saboda Shigowata Harkar Fim —Saratu Abubakar

by Bello Hamza
5 months ago
in Nishadi
0
Saratu

Sabuwar jaruma a masana’antar finafinai ta Kannywood, ta bayyana shigowar ta masana’antar da cewa lokacin ta ne ya yi don haka ba ta yi mamaki ba da ta kasance cikin wadanda a ke damawa da su a cikin harkar, saboda yadda ta dade ta na son ta yi tun ta na karama don haka sai a yanzu ne ta samu cikar burin ta na zama ‘yar fim.

Jarumar ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar mu da ita Inda take cewa, “Tsawon lokacin da na yi ina fatan na kasance ‘yar fim sai a yanzu na cika burina wanda a yanzu duk da ban dade da shigowa ba, don na fara ne a 2020 in da na fara fitowa a fim din ‘Hajiya Babba’ da ‘Ya’yan Mage’, kuma a yanzu ni ce jarumar fim din ‘Zo Mu Zauna’, kuma ina jin dadi sosai da hakan’.

  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Dangane da ko ta samu matsala daga gidan su a lokacin da ta shigo kuwa cewa ta yi, “Ai matsala sosai ma kuwa don har yanzu ina fuskantar matsalar, saboda ka san shi fim a nan kasar mu ta Hausa idan mutum ya na yi sai a rinka cewa shi dan iska ne.

To wannan ta sa har gida aka je a ke samun iyaye na ana cewa sun bar ni ina iskanci har abin ya yi musu yawa su ke ta mini magana, don haka sai nake fada musu cewa ni fa a rayuwa ta ba zan yi abin da bai dace ba, ni na san din sana’a ce kuma ita ta kawo ni, neman kudi nake yi, kuma ba wai zaman banza nake yi ba a Kano karatu nake yi sai kuma nake hadawa da fim saboda sana’a ce, don haka ba iskanci nake yi ba na dauke shi a matsayin sana’a da zan rinka yi ina rufawa kaina asiri, to haka dai suka yarda suka hakura tunda ya za su yi da ni, tunda ina cikin fim din na shiga dumu-dumu, kawai dai sai wani lokacin idan na je gida za a ce shikenan dai na shiga harkar fim ba zan yi aure ba.

Na Kano ce musu aure lokaci ne idan Allah ya kawo za a yi.”
Dangane da fim din da ta fito a matsayin Jaruma kuwa wato zo mu zauna cewa ta yi ‘Ina alfahari da fim din, domin shi ne ya fito da ni duniya ta san da ni kuma matsayin da aka ba ni na babbar Mace ya zo mini da bazata, saboda a matsayina na Budurwa da ban taba yin aure ba sai ga shi a fim na kasance matar aure har da babbar ‘ya da zan aurar da ita.

Labarai Masu Nasaba

Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara

Wannan matsayin ya daga daraja ta sai na zo ina jin kaina kamar matar aure ka ga wannan ai daukaka ce, don haka a kullum ina alfahari da fim din ‘Zo Mu Zauna.”

A game da mu’amalarta da mutane kuwa cewa ta yi ta samu ce gaba sosai.”Domin duk lokacin da na je gida, sai ka ga duk wajen da na shiga a na ta zuwa wajena don ma ba ko’ina nake shiga ba saboda duk in da ka je za a ta kallon ka”.

A game da yadda mu’amalarta take kasancewa da masoyanta kuwa cewa ta yi abin ya na burge ta saboda “Duk in da na je a na zuwa a dauki hoto da ni kuma ina samun kyauta daga wajen masoyana sannan kuma idan na shiga cikin ‘yan fim mu kan zama kamar ‘yan’uwa don ba na gane ma ba a gida nake ba saboda an hadu an zama daya, haka a ke zama a yi wasa da dariya, don yau idan ba ni da lafiya na san wanda zan kira a cikin ‘yan fim ya tsaya a kaina.

Don haka muna zama ne kamar ‘yan uwan juna.”
Daga karshe ta yi kira ga jama’a da su daina yi wa ‘yan fim kallon ‘yan iska, saboda ba kowa ba ne dan iska, don akwai mutane nagari kamar kowacce harkar, da mutanen kirki da na banza, to haka ma harkar fim take. Inji Saratu Abubakar.

Previous Post

Bayani A Game Da Sabuwar Wayar iPhone 14 (Kimiyya)

Next Post

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Related

Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe
Nishadi

Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe

1 week ago
Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara
Nishadi

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara

2 weeks ago
Iyayena Ba Su Kalubalanci Shigata Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara
Nishadi

Iyayena Ba Su Kalubalanci Shigata Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara

3 weeks ago
Abubuwan Da Suka Bambanta Harkar Fim Ta Da, Da Yanzu – Hajiya Zulaihatu
Nishadi

Abubuwan Da Suka Bambanta Harkar Fim Ta Da, Da Yanzu – Hajiya Zulaihatu

1 month ago
Akwai Raini Da Nuna Bambanci A Masana’antar Kannywood —Maman Haidar
Nishadi

Akwai Raini Da Nuna Bambanci A Masana’antar Kannywood —Maman Haidar

1 month ago
Tsokaci A Kan Karin Aure Cikin Sirri (I) (Taskira)
Nishadi

Tsokaci A Kan Karin Aure Cikin Sirri (I) (Taskira)

2 months ago
Next Post
Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

February 7, 2023
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

February 7, 2023
Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

February 7, 2023
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Dakatar Da CBN Da Buhari Ƙara Wa’adin Maye Tsoffin Kuɗi

February 6, 2023
EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

February 6, 2023
An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

February 6, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

February 6, 2023
Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

February 6, 2023
Ana Gaggauta Raya Manyan Ayyukan Ban Ruwa A Sassan Kasar Sin

Ana Gaggauta Raya Manyan Ayyukan Ban Ruwa A Sassan Kasar Sin

February 6, 2023
Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

February 6, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.