ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

by Rabi'at Sidi Bala
4 years ago
Kannywood

Daya daga cikin mawaka kuma Jarumi a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood wato YUNUSA MUHAMMAD GAYA, ya bayyana wa masu karatu dalilin da ya sa ya tsunduma harkar fim da waka, inda ya yi kira ga Mawaka da Jarumai su guji isar da sakon da bai dace ba. Ya kuma bayyana irin mukaman da ya rike game da wannan sana’a tasa, har da wasu batutuwan da suka shafi sana’arsa ta fim da waka. Ga dai tattaunawar tare da wakilinmu YAKUBU FURODUSA GWAMMAJA Kamar haka:

Masu karatu za su so su ji cikakken sunanka…
Sunana Yunusa Muhammad Gaya Shugaban Kundin Muryar Mawakan Arewa.

Ko za ka fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?
Ni dan Karamar Hukumar Gaya ne, Kano, Almajiri ne ni bayan na samu haddar Alkur’ani na yi karatun sakandare a Gwale, yanzu ina karatun gaba da sakandare a Sa’adatu Rimi. Na Jagoranci Kungiyar Sha’irai ta Gaya shekara 12, na jagoranci Kungiyar mawalfa ta Gaya shekara 8, na rike ma’aji na kungiyar mawallafa na Jihar Kano. Shekra 2 na rike ma’aji na kundin muryar Mawakan Arewa, yanzu haka ni ne shugabanta na kasa yau shekara 6, na taba samun gwarzon shekara na yabon manzon Allah (SAW) na Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Kannywood

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma harkar waka?
Na shiga harkar waka ne don isar da sako zuwa ga al’umma, na wa’azantarwa. Haka zalika na shiga harkar fm don fito da martabar al’adata da kuma fadakarwa.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Bayan waka har fim kana yi kenan?
Eh ina yin fim.

Da wanne fim ka fara?
Wani fim ne ‘Me Zai Faru’. Fim din dana fara nawa shi ne;
BA DA NI BA, wanda ya ba da umarni Yakubu Producer. Ma’anar fim din duk wani abin ki jaruman ciki za ka ji na kira ba da ni ba.

Wacce waka ce ta zama bakandamiyarka?
Har yanzu ban fid da bakandamiyar wakata ba.

Nawa ne adadin fina-finan da ka yi da kuma wakoki?
Fina-finaina ba su wuce guda 6 ba, wakoki kuma ba zan iya kidaya su ba duba da mawakan kowanne ban gare ne ni na Hausa.

Za ka yi kamar shekara nawa cikin masana’antar?
Na shiga masana’antar ina da shekara 19.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?
Hakika an yi gwagwarmaya sosai don harka ce da take bukatar ka san mafi yawan wanda ke da alaka da harkar, sannan harka ce da ke bukatar hakuri.

Wanne irin kalubale ka taba fuskanta game da wannan sana’a taka?
Alhamdulillah kalubale ba za a ce babu ba, musamman a harkar jagoranci duba da kullum burina ya za ayi na samarwa ‘yan kungiyar mafita.

Ya batun nasarori fa?
Ma Sha Allahu na samu nasarori sosai ba zan iya kididdige su ba na kuma yi alaka da manyan mutane da dama.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ka taba mantawa da shi ba?
Abin da ya taba faruwa da ni sanadin harkar, suna da yawa mafi zamammin a rai shi ne kyautar fili da samamin aikin gwamnati.

Kannywood
Yunusa tare da Hadiza Kabara

Wane ne babban abokinka a cikin masana’antar?
Ina da abokai da yawa wadanda kullum ba ma rabuwa.

Da wa ka fi so a hada ka a fim?
Ba ni da zabi a kan wacce na fi so a hada mu a fim.

Mene ne burinka game da waka?
Burina shi ne na ga Al’umma na alfahari da wakokina da kuma fim dina ina so kuma na taimaki na kasa da ni a kan harkar, duk da ba wani girma na yi a ciki ba.

Ya ka dauki harkar waka a wajenka?
Na dauki harkar waka sana’a da kuma harkar fim, sannan wata hanya ce ta kai sako ga al’umma.

Bayan fim da waka kana da wata sana’ar ne, in akwai ya kake iya hada kasuwancinka da kuma sana’arka da fim da waka?
Ina da sana’a na kan iya ware lokacin kasuwaci, ina iya ware lokacin harkar waka ko fim.

To ya batun soyayya fa, ko akwai wadda ta taba kwanta maka a rai cikin masana’antar da har ta kai kun fara soyayya?
Ban fara soyayya ba, amma in hakan ta kama ba zan ki ba, duba da na yi nasarar hada auran ‘yar fim da dan fim ko mawaki da mawakiya ya kai guda 5.

Yaushe za ka yi aure?
Ina da aure matana 2 yanzu haka, ina kokarin karawa in sha Allah.

Wanne kira za kai wa masu kokarin shiga harkar fim?
Kirana ga musu sha’awar shiga harkar shi ne; Kai kokarin ka shigo da kyakyawar manufa.

Wanne kira za ka yi ga sauran abokan sana’arka?
Kirana ga abokan sana’ar mawaka da jarumai, don Allah mu guje wa isar da sakon da bai kamata ba mu kuma kaunaci juna.

Ko kana da wani kira da za ka yi ga gwamnati game da wannan harka taka ta wakoki?
Kirana ga hukuma ta yi kokarin shiga harkar waka ba harkar gudummawa da kara kokarin wajen tantance harkar.

Kannywood

Me za ka ce game da Jaridar Leadership Hausa?
Ina godiya ga jaridar Leadership Hausa,
Allah ya kara daukaka ku dari bisa dari.

Muna godiya
Ni ma na gode.

Kannywood
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Kannywood
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Tambuwal Ya Yi Ganawar Sirri Da Obasanjo

Tambuwal Ya Yi Ganawar Sirri Da Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.