• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Bandung

Yau dai sama da shekaru 70 da suka wuce ke nan da wasu kasashen Asiya da Afirka suka bude babin yakar mulkin mallaka da ra’ayin nuna fin karfi bisa ruhin taron Bandung da ya yi kiran “hadin kai da sada zumunta da hadin gwiwa”, taron da ya samu halartar kasashe 29 na Asiya da Afirka, wanda ya gudana a birnin Bandung na kasar Indonesia. A zamanin da muke ciki kuma, kasashe masu tasowa na ci gaba da rungumar ruhin taron, a kokarinsu na gyara tsarin duniya, wato a kafa tsarin da ke tabbatar da bunkasar kasa da kasa ta bai daya, tare da yin watsi da tsohon tsarin da kasashe masu karfi ke cin zalin kasashe masu karamin karfi.

 

A gun taron Bandung, wakilin kasar Sin ya jaddada cewa, “kamata ya yi kasa da kasa komai karfinsu su yi zaman daidaito da juna”, furucin da ba kawai ya yi watsi da mulkin mallaka ba ne, hatta ma da irin yadda kasashe masu ci gaba ke nuna fin karfi a harkokin duniya. A gwagwarmayar da kasashe masu tasowa suka yi cikin shekaru 70 da suka wuce, sun karya lagon babakeren da aka kafa ta dalar Amurka, inda kasashen Brazil da Sin suka yi cinikin waken soya da kudadensu, kuma India ta sayi man Iran da kudinta na Rupee, kasashen Afirka ma na kokarin sa kaimin kafa tsarin ciniki na kudadensu a yankin ciniki marar shinge na nahiyar, matakan da suka sa kason cinikin da aka yi da dala ya ragu daga kashi 73% a shekarar 2001 zuwa kashi 49% a yanzu. Baya ga haka, kasashen sun kuma karya babakeren da aka yi ta fannin kimiyya da fasaha, inda kasar Sin ta fitar da samfurin kirkirarriyar basira ta Deepseek, kuma Masar ta kafa masana’antar samar da motocin lantarki ta farko a Afirka…… A sa’i daya kuma, kasashen sun kara fitowa da muryoyinsu a duniya, duba da cewa, tarayyar Afirka ta sa kaimin ganin gyare-gyaren hukumomin hada-hadar kudi na duniya bayan da aka shigar da ita kungiyar G20, kuma a gun shawarwari kan sauyin yanayin duniya kungiyar G77 ta bukaci kasashen yamma su biya diyyar hasarorin da suka sha……

 

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai wasu kasashe uku na kudu maso gabashin Asiya a wannan mako, ta kuma kara shaida yadda ake ci gaba da rungumar ruhin taron Bandung. A ziyararsa a Vietnam, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa har 45, tare da fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, za a yayata akidun zaman lafiya da ci gaba da adalci da dimokuradiyya da ‘yanci da baki dayan dan Adam ke rungumarsu, tare da nuna goyon baya ga bunkasar kasashe daban daban da kuma dunkulewar tattalin arzikin duniya. A Malaysia kuma, kasashen biyu sun fitar da sanarwar hadin gwiwa da ke cewa, za su karfafa hadin gwiwarsu ta fannin more damammaki da tabbatar da ci gaba da tinkarar kalubale da kiyaye tsaro, tare da bayar da karin gudummawarsu wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali da inganta tsarin hadin gwiwa a shiyyar. Har ila yau, a kasar Cambodia kuma, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa ta fannin aiwatar da ayyuka masu alaka da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, baya ga hadaddiyar sanarwar da suka fitar ta jaddada muhimmancin “ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana” da kuma ruhin taron Bandung. Wadannan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da suka cimma da sanarwoyin da suka fitar duk sun shaida ainihin sakon da taron Bandung ke fatan isarwa, wato hakkin ci gaba shi ne hakkin dan Adam mafi muhimmanci, kuma ‘yancin gudanar da harkoki na kashin kanta shi ne tushen ikon mulkin kai na duk wata kasa, kuma matukar kasa da kasa suka zama tsintsiya madaurinki guda za su iya tinkarar kalubalen da ke gabansu.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

 

A shekaru 70 da suka wuce, kasashen yamma sun yi wa taron Bandung kallon taro na kasashe matalauta, amma kuma ga irin yadda ya haifar da kyakkyawan sakamako ga mikewar kasashen. A zamanin yau, lokacin da kasar Amurka ke ta kara kakaba harajin kwastam a kan sauran kasashen duniya, muna farin cikin ganin yadda kasashe masu tasowa ke hada kansu, da rike tsaronsu da ci gabansu a hannunsu, suna kuma rungumar akidun zaman lafiya da hadin gwiwa da bude kofa don tinkarar yadda kasashe masu karfi ke neman cin zalin kasashe masu karamin karfi da ma rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Yau da muke waiwayen taron Bandung, za mu gano cewa, ko-ba-dade-ko-ba-jima za mu ga bayan nuna fin karfi a tarihin wayewar kan dan Adam. (Lubabatu)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Next Post
Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.