ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Bandung

Yau dai sama da shekaru 70 da suka wuce ke nan da wasu kasashen Asiya da Afirka suka bude babin yakar mulkin mallaka da ra’ayin nuna fin karfi bisa ruhin taron Bandung da ya yi kiran “hadin kai da sada zumunta da hadin gwiwa”, taron da ya samu halartar kasashe 29 na Asiya da Afirka, wanda ya gudana a birnin Bandung na kasar Indonesia. A zamanin da muke ciki kuma, kasashe masu tasowa na ci gaba da rungumar ruhin taron, a kokarinsu na gyara tsarin duniya, wato a kafa tsarin da ke tabbatar da bunkasar kasa da kasa ta bai daya, tare da yin watsi da tsohon tsarin da kasashe masu karfi ke cin zalin kasashe masu karamin karfi.

 

A gun taron Bandung, wakilin kasar Sin ya jaddada cewa, “kamata ya yi kasa da kasa komai karfinsu su yi zaman daidaito da juna”, furucin da ba kawai ya yi watsi da mulkin mallaka ba ne, hatta ma da irin yadda kasashe masu ci gaba ke nuna fin karfi a harkokin duniya. A gwagwarmayar da kasashe masu tasowa suka yi cikin shekaru 70 da suka wuce, sun karya lagon babakeren da aka kafa ta dalar Amurka, inda kasashen Brazil da Sin suka yi cinikin waken soya da kudadensu, kuma India ta sayi man Iran da kudinta na Rupee, kasashen Afirka ma na kokarin sa kaimin kafa tsarin ciniki na kudadensu a yankin ciniki marar shinge na nahiyar, matakan da suka sa kason cinikin da aka yi da dala ya ragu daga kashi 73% a shekarar 2001 zuwa kashi 49% a yanzu. Baya ga haka, kasashen sun kuma karya babakeren da aka yi ta fannin kimiyya da fasaha, inda kasar Sin ta fitar da samfurin kirkirarriyar basira ta Deepseek, kuma Masar ta kafa masana’antar samar da motocin lantarki ta farko a Afirka…… A sa’i daya kuma, kasashen sun kara fitowa da muryoyinsu a duniya, duba da cewa, tarayyar Afirka ta sa kaimin ganin gyare-gyaren hukumomin hada-hadar kudi na duniya bayan da aka shigar da ita kungiyar G20, kuma a gun shawarwari kan sauyin yanayin duniya kungiyar G77 ta bukaci kasashen yamma su biya diyyar hasarorin da suka sha……

ADVERTISEMENT

 

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai wasu kasashe uku na kudu maso gabashin Asiya a wannan mako, ta kuma kara shaida yadda ake ci gaba da rungumar ruhin taron Bandung. A ziyararsa a Vietnam, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa har 45, tare da fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, za a yayata akidun zaman lafiya da ci gaba da adalci da dimokuradiyya da ‘yanci da baki dayan dan Adam ke rungumarsu, tare da nuna goyon baya ga bunkasar kasashe daban daban da kuma dunkulewar tattalin arzikin duniya. A Malaysia kuma, kasashen biyu sun fitar da sanarwar hadin gwiwa da ke cewa, za su karfafa hadin gwiwarsu ta fannin more damammaki da tabbatar da ci gaba da tinkarar kalubale da kiyaye tsaro, tare da bayar da karin gudummawarsu wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali da inganta tsarin hadin gwiwa a shiyyar. Har ila yau, a kasar Cambodia kuma, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa ta fannin aiwatar da ayyuka masu alaka da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, baya ga hadaddiyar sanarwar da suka fitar ta jaddada muhimmancin “ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana” da kuma ruhin taron Bandung. Wadannan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da suka cimma da sanarwoyin da suka fitar duk sun shaida ainihin sakon da taron Bandung ke fatan isarwa, wato hakkin ci gaba shi ne hakkin dan Adam mafi muhimmanci, kuma ‘yancin gudanar da harkoki na kashin kanta shi ne tushen ikon mulkin kai na duk wata kasa, kuma matukar kasa da kasa suka zama tsintsiya madaurinki guda za su iya tinkarar kalubalen da ke gabansu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

 

A shekaru 70 da suka wuce, kasashen yamma sun yi wa taron Bandung kallon taro na kasashe matalauta, amma kuma ga irin yadda ya haifar da kyakkyawan sakamako ga mikewar kasashen. A zamanin yau, lokacin da kasar Amurka ke ta kara kakaba harajin kwastam a kan sauran kasashen duniya, muna farin cikin ganin yadda kasashe masu tasowa ke hada kansu, da rike tsaronsu da ci gabansu a hannunsu, suna kuma rungumar akidun zaman lafiya da hadin gwiwa da bude kofa don tinkarar yadda kasashe masu karfi ke neman cin zalin kasashe masu karamin karfi da ma rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Yau da muke waiwayen taron Bandung, za mu gano cewa, ko-ba-dade-ko-ba-jima za mu ga bayan nuna fin karfi a tarihin wayewar kan dan Adam. (Lubabatu)

 

Bandung
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Bandung
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Bandung

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bandung

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.