ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Bandung

Yau dai sama da shekaru 70 da suka wuce ke nan da wasu kasashen Asiya da Afirka suka bude babin yakar mulkin mallaka da ra’ayin nuna fin karfi bisa ruhin taron Bandung da ya yi kiran “hadin kai da sada zumunta da hadin gwiwa”, taron da ya samu halartar kasashe 29 na Asiya da Afirka, wanda ya gudana a birnin Bandung na kasar Indonesia. A zamanin da muke ciki kuma, kasashe masu tasowa na ci gaba da rungumar ruhin taron, a kokarinsu na gyara tsarin duniya, wato a kafa tsarin da ke tabbatar da bunkasar kasa da kasa ta bai daya, tare da yin watsi da tsohon tsarin da kasashe masu karfi ke cin zalin kasashe masu karamin karfi.

 

A gun taron Bandung, wakilin kasar Sin ya jaddada cewa, “kamata ya yi kasa da kasa komai karfinsu su yi zaman daidaito da juna”, furucin da ba kawai ya yi watsi da mulkin mallaka ba ne, hatta ma da irin yadda kasashe masu ci gaba ke nuna fin karfi a harkokin duniya. A gwagwarmayar da kasashe masu tasowa suka yi cikin shekaru 70 da suka wuce, sun karya lagon babakeren da aka kafa ta dalar Amurka, inda kasashen Brazil da Sin suka yi cinikin waken soya da kudadensu, kuma India ta sayi man Iran da kudinta na Rupee, kasashen Afirka ma na kokarin sa kaimin kafa tsarin ciniki na kudadensu a yankin ciniki marar shinge na nahiyar, matakan da suka sa kason cinikin da aka yi da dala ya ragu daga kashi 73% a shekarar 2001 zuwa kashi 49% a yanzu. Baya ga haka, kasashen sun kuma karya babakeren da aka yi ta fannin kimiyya da fasaha, inda kasar Sin ta fitar da samfurin kirkirarriyar basira ta Deepseek, kuma Masar ta kafa masana’antar samar da motocin lantarki ta farko a Afirka…… A sa’i daya kuma, kasashen sun kara fitowa da muryoyinsu a duniya, duba da cewa, tarayyar Afirka ta sa kaimin ganin gyare-gyaren hukumomin hada-hadar kudi na duniya bayan da aka shigar da ita kungiyar G20, kuma a gun shawarwari kan sauyin yanayin duniya kungiyar G77 ta bukaci kasashen yamma su biya diyyar hasarorin da suka sha……

ADVERTISEMENT

 

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai wasu kasashe uku na kudu maso gabashin Asiya a wannan mako, ta kuma kara shaida yadda ake ci gaba da rungumar ruhin taron Bandung. A ziyararsa a Vietnam, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa har 45, tare da fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, za a yayata akidun zaman lafiya da ci gaba da adalci da dimokuradiyya da ‘yanci da baki dayan dan Adam ke rungumarsu, tare da nuna goyon baya ga bunkasar kasashe daban daban da kuma dunkulewar tattalin arzikin duniya. A Malaysia kuma, kasashen biyu sun fitar da sanarwar hadin gwiwa da ke cewa, za su karfafa hadin gwiwarsu ta fannin more damammaki da tabbatar da ci gaba da tinkarar kalubale da kiyaye tsaro, tare da bayar da karin gudummawarsu wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali da inganta tsarin hadin gwiwa a shiyyar. Har ila yau, a kasar Cambodia kuma, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa ta fannin aiwatar da ayyuka masu alaka da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, baya ga hadaddiyar sanarwar da suka fitar ta jaddada muhimmancin “ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana” da kuma ruhin taron Bandung. Wadannan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da suka cimma da sanarwoyin da suka fitar duk sun shaida ainihin sakon da taron Bandung ke fatan isarwa, wato hakkin ci gaba shi ne hakkin dan Adam mafi muhimmanci, kuma ‘yancin gudanar da harkoki na kashin kanta shi ne tushen ikon mulkin kai na duk wata kasa, kuma matukar kasa da kasa suka zama tsintsiya madaurinki guda za su iya tinkarar kalubalen da ke gabansu.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

 

A shekaru 70 da suka wuce, kasashen yamma sun yi wa taron Bandung kallon taro na kasashe matalauta, amma kuma ga irin yadda ya haifar da kyakkyawan sakamako ga mikewar kasashen. A zamanin yau, lokacin da kasar Amurka ke ta kara kakaba harajin kwastam a kan sauran kasashen duniya, muna farin cikin ganin yadda kasashe masu tasowa ke hada kansu, da rike tsaronsu da ci gabansu a hannunsu, suna kuma rungumar akidun zaman lafiya da hadin gwiwa da bude kofa don tinkarar yadda kasashe masu karfi ke neman cin zalin kasashe masu karamin karfi da ma rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Yau da muke waiwayen taron Bandung, za mu gano cewa, ko-ba-dade-ko-ba-jima za mu ga bayan nuna fin karfi a tarihin wayewar kan dan Adam. (Lubabatu)

 

Bandung
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Bandung
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.